• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Takarda Ta Nuna Tushen Manufar Kasar Sin

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wannan Takarda Ta Nuna Tushen Manufar Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, a ganinku, me ya kamata a ce takardar farko da mahukuntan wata kasa su kan gabatar a duk shekara ta kunsa?

A kwanakin nan, kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da majalisar gudanarwar kasar suka gabatar da Takarda Mai Lamba 1 ta bana, wadda ta shafi ayyuka masu alaka da aikin gona, da raya kauyuka, gami da manoma. Shekaru 21 a jere ke nan da shugabannin kasar Sin suka gabatar da takarda ta farko a shekara da ta shafi wannan jigo.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Cinikayyar Hayakin Carbon
  • CMG Ya Shirya Shagali Gabanin Liyafar Bikin Bazara A Geneva

To, sai dai me ya sa ake daukar aikin gona, da kauyuka, da manoma da matukar muhimmanci a kasar Sin?

Saboda da sai da aikin gona mai inganci ne ake iya tabbatar da cewa al’ummar kasar Sin fiye da biliyan 1.4 suke iya samun isasshen abincin da suke bukata. Kana kauyuka a nasu bangare, ba su kai birane a fannin ci gaban tattalin arziki ba, don haka dole ne a ba su karin tallafi. Yayin da ingancin rayuwar manoma ke zama wani muhimmin bangare da zai tabbatar da samun daidaito tsakanin al’umma, inda dukkansu za a wadatar da su a kasar ta Sin.

Wato ana mai da hankali kan aikin gona, da kauyuka da manoma a kasar Sin ne domin neman tabbatar da ci gaban kasa mai dorewa kuma cikin daidaito, da samun ingantuwar rayuwar jama’a a kai a kai. Sa’an nan tushen wadannan manufofi shi ne tunanin shugabannin kasar Sin na “Mai da jama’a gaban kome. ”

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Wannan tunani ya yi tasiri kan manufofin kasar Sin na cikin gida da na waje. Saboda haka gwamnatin kasar tana raya aikin gona, da harkoki masu alaka da kauyuka da manoma a cikin gida, gami da neman gina “al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya” a duniya, inda take kokarin haifar da ci gaba a sauran kasashe masu tasowa.

A kasar Sin, don ganin an tabbatar da samar da isashen abinci, ana ta kokarin fito da sabbin fasahohin aikin gona da za su tabbatar da samun girbi mai armashi a gonaki. Yayin da a jihar Morogoro ta kasar Tanzania, wasu kwararru Sinawa sun yi kokarin yada fasaha mai inganci ta shuka masara, cikin shekarun da suka gabata, inda har yawan masarar da ake girbi a can ya ninka sau 3.

Ban da haka, a lardin Zhejiang na kasar Sin da na taba ziyarta, na ga yadda kauyuka su ke raya sana’ar da ta dace da albarkatunsu. Misali a kan yi kiwon kifi a wuraren dake dab da tabkuna, da raya aikin yawon shakatawa a wurare masu duwatsu. Sa’an nan, a kasar Kongo Brazaville, ana yawan noman rogo, wanda yake lalacewa da wuri yayin da ake ajiyewa da jigilarsu. Saboda haka, bisa la’akari da yanayin da ake ciki wajen gudanar da aikin gona a Kongo Brazaville, da bukatar dake akwai, Sinawa sun samar da wasu injuna na sarrafa rogo, inda ake nika shi zuwa gari a kasar, matakin da ya taimaka wajen raya masana’antu, baya ga taimakawa manoma samun karin kudin shiga.

Haka zalika a wani kauye mai suna Ping Di Cun dake kudancin birnin Beijing na kasar Sin, na ga yadda gwamnatin wurin ta zuba kudade, tare da dasa itatuwa, da gina wuraren shakatawa, da sabbin ban dakuna, don inganta zaman rayuwar mazauna kauyen. Yayin da a Najeriya, wani kamfanin sadarwa na kasar Sin shi ma ya saukaka zaman rayuwar manoma, inda injiniyoyinsa suka yi amfani da itatuwa wajen kafa ginshikai masu dauke da na’urar samar da wutar lantarki ta hasken rana, da na’urorin sadarwa, ta yadda hakan ya taimaki mazauna kauyuka wajen magance matsalolin sadarwa, ban da wannan kuma, an ba su damar cajin wayoyin salularsu kyauta.

Bisa wadannan misalai muna iya ganin cewa, manufofin kasar Sin na cikin gida da na hulda da kasashen waje suna da tushe iri daya, wato tunani na mai da hakki da moriyar jama’a gaban kome. Wannan ma wani dalili ne da ya sa ake iya tabbatar da gaskiya, da kauna, da nuna sahihanci, gami da samar da hakikanin sakamako, yayin da ake gudanar da hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CMGKamfanin yada labarai na SinLiyafar cin abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yankewa Wata Uwargida A Kano Hukuncin Ɗaurin Rai-da-rai Kan Mutuwar Ɗan Kishiyarta

Next Post

Yawan Mutanen Da Ake Jigila A Bikin Bazara Ya Bayyana Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Related

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

1 hour ago
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

2 hours ago
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

3 hours ago
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

22 hours ago
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

23 hours ago
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

1 day ago
Next Post
Yawan Mutanen Da Ake Jigila A Bikin Bazara Ya Bayyana Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Yawan Mutanen Da Ake Jigila A Bikin Bazara Ya Bayyana Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Kwanciyar Aure

Yadda Hadarin Mutuwa Ke Karuwa Yayin Ko Bayan Saduwa Da Iyali

July 26, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

July 26, 2025
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

July 26, 2025
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.