• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Takarda Ta Nuna Tushen Manufar Kasar Sin

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wannan Takarda Ta Nuna Tushen Manufar Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, a ganinku, me ya kamata a ce takardar farko da mahukuntan wata kasa su kan gabatar a duk shekara ta kunsa?

A kwanakin nan, kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da majalisar gudanarwar kasar suka gabatar da Takarda Mai Lamba 1 ta bana, wadda ta shafi ayyuka masu alaka da aikin gona, da raya kauyuka, gami da manoma. Shekaru 21 a jere ke nan da shugabannin kasar Sin suka gabatar da takarda ta farko a shekara da ta shafi wannan jigo.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Cinikayyar Hayakin Carbon
  • CMG Ya Shirya Shagali Gabanin Liyafar Bikin Bazara A Geneva

To, sai dai me ya sa ake daukar aikin gona, da kauyuka, da manoma da matukar muhimmanci a kasar Sin?

Saboda da sai da aikin gona mai inganci ne ake iya tabbatar da cewa al’ummar kasar Sin fiye da biliyan 1.4 suke iya samun isasshen abincin da suke bukata. Kana kauyuka a nasu bangare, ba su kai birane a fannin ci gaban tattalin arziki ba, don haka dole ne a ba su karin tallafi. Yayin da ingancin rayuwar manoma ke zama wani muhimmin bangare da zai tabbatar da samun daidaito tsakanin al’umma, inda dukkansu za a wadatar da su a kasar ta Sin.

Wato ana mai da hankali kan aikin gona, da kauyuka da manoma a kasar Sin ne domin neman tabbatar da ci gaban kasa mai dorewa kuma cikin daidaito, da samun ingantuwar rayuwar jama’a a kai a kai. Sa’an nan tushen wadannan manufofi shi ne tunanin shugabannin kasar Sin na “Mai da jama’a gaban kome. ”

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Wannan tunani ya yi tasiri kan manufofin kasar Sin na cikin gida da na waje. Saboda haka gwamnatin kasar tana raya aikin gona, da harkoki masu alaka da kauyuka da manoma a cikin gida, gami da neman gina “al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya” a duniya, inda take kokarin haifar da ci gaba a sauran kasashe masu tasowa.

A kasar Sin, don ganin an tabbatar da samar da isashen abinci, ana ta kokarin fito da sabbin fasahohin aikin gona da za su tabbatar da samun girbi mai armashi a gonaki. Yayin da a jihar Morogoro ta kasar Tanzania, wasu kwararru Sinawa sun yi kokarin yada fasaha mai inganci ta shuka masara, cikin shekarun da suka gabata, inda har yawan masarar da ake girbi a can ya ninka sau 3.

Ban da haka, a lardin Zhejiang na kasar Sin da na taba ziyarta, na ga yadda kauyuka su ke raya sana’ar da ta dace da albarkatunsu. Misali a kan yi kiwon kifi a wuraren dake dab da tabkuna, da raya aikin yawon shakatawa a wurare masu duwatsu. Sa’an nan, a kasar Kongo Brazaville, ana yawan noman rogo, wanda yake lalacewa da wuri yayin da ake ajiyewa da jigilarsu. Saboda haka, bisa la’akari da yanayin da ake ciki wajen gudanar da aikin gona a Kongo Brazaville, da bukatar dake akwai, Sinawa sun samar da wasu injuna na sarrafa rogo, inda ake nika shi zuwa gari a kasar, matakin da ya taimaka wajen raya masana’antu, baya ga taimakawa manoma samun karin kudin shiga.

Haka zalika a wani kauye mai suna Ping Di Cun dake kudancin birnin Beijing na kasar Sin, na ga yadda gwamnatin wurin ta zuba kudade, tare da dasa itatuwa, da gina wuraren shakatawa, da sabbin ban dakuna, don inganta zaman rayuwar mazauna kauyen. Yayin da a Najeriya, wani kamfanin sadarwa na kasar Sin shi ma ya saukaka zaman rayuwar manoma, inda injiniyoyinsa suka yi amfani da itatuwa wajen kafa ginshikai masu dauke da na’urar samar da wutar lantarki ta hasken rana, da na’urorin sadarwa, ta yadda hakan ya taimaki mazauna kauyuka wajen magance matsalolin sadarwa, ban da wannan kuma, an ba su damar cajin wayoyin salularsu kyauta.

Bisa wadannan misalai muna iya ganin cewa, manufofin kasar Sin na cikin gida da na hulda da kasashen waje suna da tushe iri daya, wato tunani na mai da hakki da moriyar jama’a gaban kome. Wannan ma wani dalili ne da ya sa ake iya tabbatar da gaskiya, da kauna, da nuna sahihanci, gami da samar da hakikanin sakamako, yayin da ake gudanar da hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CMGKamfanin yada labarai na SinLiyafar cin abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yankewa Wata Uwargida A Kano Hukuncin Ɗaurin Rai-da-rai Kan Mutuwar Ɗan Kishiyarta

Next Post

Yawan Mutanen Da Ake Jigila A Bikin Bazara Ya Bayyana Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

1 hour ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

2 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

4 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

7 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

8 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

9 hours ago
Next Post
Yawan Mutanen Da Ake Jigila A Bikin Bazara Ya Bayyana Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Yawan Mutanen Da Ake Jigila A Bikin Bazara Ya Bayyana Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.