• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Sabuwar Cuta Ta Kashe Yara 10 ‘Yan Kasa Da Shekara 13 A Kaduna 

by Sulaiman
2 years ago
Cuta

Kimanin yara 10 ne ‘yan tsakanin shekaru 3 zuwa 13 aka rahoto sun rasa rayukansu sakamakon bullar wata cuta mai shake numfashi a garin Kafanchan da ke karamar hukumar Jema’a ta jihar Kaduna.

Babban Daraktan lafiya (CMD) na asibitin ‘Sir Patrick Ibrahim Yakowa’, Dakta Isaac Nathaniel ne ya tabbatar da bullar cutar a Kafanchan inda ya ce har yanzun ba a gano musabbabin cutar ba.

  • Sojoji Sun Yi Nasarar Kashe ‘Yan Ta’adda 6 Da Kwato Makamai Da Dama A Kaduna

Shugaban Karamar Hukumar Jema’a ta Jihar Kaduna, Honarabul Yunana Markus Barde, ya yi kira ga mazauna garin da su tashi tsaye sukai rahoton duk wani yaro mai shekaru kasa da 13 da ke fama da matsalar shakewar numfashi, ciwon makogwaro ko kuma yoyon majina a hanci ga hukumomin kiwon lafiya mafi kusa.

Shugaban ya bukaci mazauna garin da su lura da irin wadannan alamomin domin dakile yaduwar cutar da wuri kafin ta yi kamari.

Haka kuma an shawarci ma’aikatan kiwon lafiya a matakin farko a fadin kananan hukumomi, cibiyoyin maganin gargajiya, malaman addini, da iyaye da su dauki matakin da ya dace, ganin cewa, wasu iyaye da ‘yan uwa suna boye wasu daga cikin masu fama da cutar.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Ya ja hankali cewa, masu wannan dabi’a, sam hakan bai dace ba, annoba ta kan zama illa ga duk al’umma baki daya idan ba a hada guiwa an yake ta ba.

Daktan ya kara da cewa, kwararru daga babban birnin tarayya Abuja da jihar Kaduna za su zo garin domin kawo dauki, ya bukaci al’ummar karamar hukumar Jema’a da su bayyana duk wanda aka ga yana dauke da irin alamomin cutar ga hukumar lafiya ta matakin farko, da cibiyoyin gargajiya da sauran hukumomin da abin ya shafa domin gaggauta daukar mataki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba
Labarai

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Next Post
Jarin Waje Da Kamfanonin Sin Suka Zuba A Kasashen Waje Ya Karu A Watanni Shida Na Farkon Bana

Jarin Waje Da Kamfanonin Sin Suka Zuba A Kasashen Waje Ya Karu A Watanni Shida Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.