Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a kara kokari wajen ganin an zamanantar da karfi da tsarin tsaron kasar.
Xi Jinping ya bayyana haka ne lokacin da yake jagorantar taro karo na farko, na hukumar tsaron kasa, karkashin kwamitin kolin JKS na 20.
Xi Jinping wanda shi ne shugaban hukumar, ya yi kira da kasance cikin sani da fahimtar yanayi mai sarkakkiya da kalubale da tsaron kasa ke fuskanta, da kuma tunkarar manyan batutuwan tsaro yadda ya kamata.
Ya kuma bukaci a kiyaye sabon salon ci gaban kasar ta hanyar sabon tsarin tsaro da samun sabbin ci gaba a fannin aikin tsaron kasa. (Fa’iza)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp