• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken, a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing na kasar Sin.

A yayin ganawar, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, ya kamata Sin da Amurka su zama abokai, a maimakon abokan gaba, kana su samu bunkasuwa tare, a maimakon kawo matsala ga juna, da neman ra’ayi daya da amincewa da bambance-bambancensu, a maimakon yin mugun takara da juna, da kuma cika alkawarinsu.

  • Yanzu-yanzu: Wasu Magina Sun Makale A Baraguzan Wani Gini Da Ya Rushe A Kano
  • An Kaddamar Da Bikin Nune-nunen Shirye-shiryen Bidiyo Da Sinima Na Kasar Sin A Kasar Serbia

Shugaba Xi ya jaddada cewa, kasar Sin a shirye take ta yi hadin gwiwa da bangarorin da suke son yin hadin gwiwa da ita. Sin ba ta jin tsoron yin takara, amma ya kamata a yi hakan don samun bunkasuwa tare, a maimakon cin moriya da faduwar wani. Kana kasar Sin ta tsaya tsayin daka kan kauracewa kafa kawance, kuma tana fatan Amurka ba za ta kafa kawancenta, da nufin yin adawa da Sin ba. Bangarorin biyu suna da abokan huldarsu, amma babu bukatar nuna kiyayya da juna da kawo matsaloli ga juna.

A nasa bangare, Blinken ya bayyana cewa, a halin yanzu, ana fuskantar kalubale mai sarkakiya a duniya, ana bukatar Amurka da Sin su yi hadin gwiwa wajen tinkarar kalubalen tare. A yayin ziyararsa a kasar Sin, ya gano bangarori daban daban na Amurka dake kasar Sin suna son kyautata dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin. Amurka ba za ta ta da sabon yakin cacar baka, da canja tsarin kasar Sin, da dakile bunkasuwar kasar Sin, da kin amincewa da Sin ta hanyar kafa kawance, da kuma ta da rikici da kasar Sin ba. Amurka ta tsaya tsayin daka kan manufar “Sin daya tak a duniya”, kana tana son kiyaye yin mu’amala da kasar Sin, da aiwatar da matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma a birnin Los Angeles, da neman karin hadin gwiwa, da magance rashin fahimtar juna, da daidaita matsalolinsu, ta hakan za a sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin yadda ya kamata.

Yau Jumma’a, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi shawarwari da takwaransa na kasar Amurka Antony Blinken a birnin Beijing, a ci gaba da ziyarar aiki da mista Blinken din ke yi a nan kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

Yayin zantawarsu, Wang Yi ya yi tsokaci kan huldar kasashen biyu. A cewarsa, huldar kasashen biyu tana dan kara kyautata karkashin jagorancin shugabannin kasashen biyu, amma a wani bangare na daban, wasu abubuwan dake kawo cikas ga huldarsu na kara karuwa.

Wang, ya kuma jadadda cewa, Sin na tsayawa kan raya huldar kasashen biyu bisa ra’ayin kafa kyakkyawar makomar bil Adama ta bai daya, kuma tana tsayawa tsayin daka kan ka’idar da Xi Jinping ya gabatar, wato mutunta juna, da zama tare cikin lumana, da hadin kai, da cin moriya tare.

Kaza lika, Sin na fatan bangarorin biyu za su mai da hankali kan muradun da suka fi jawo hankalinsu, da fatan Amurka za ta kaucewa tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, da yiwa bunkasuwar Sin matsin lamba. Kana ta kauracewa keta tushen muradun Sin, wato bangaren ikon mulkin kasar, da tsaro da bunkasuwa. (Zainab Zhang&Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fara Aikin Matatar Dangote Da Ta Fatakwal: Jama’a Na Dokin Karyewar Farashin Fetur

Next Post

Zaman Lafiya: Malaman Kirista Na Arewa Sun Ziyarci Khalifa Sanusi Na II

Related

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
Daga Birnin Sin

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

8 hours ago
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu
Daga Birnin Sin

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

9 hours ago
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
Daga Birnin Sin

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

10 hours ago
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

12 hours ago
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

14 hours ago
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu
Daga Birnin Sin

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

15 hours ago
Next Post
Sanusi

Zaman Lafiya: Malaman Kirista Na Arewa Sun Ziyarci Khalifa Sanusi Na II

LABARAI MASU NASABA

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

May 31, 2025
Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

May 30, 2025
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

May 30, 2025
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

May 30, 2025
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.