ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Isa Hanoi A Ziyarar Aiki Da Ya Fara A Kasar Vietnam

by CGTN Hausa
2 years ago
xi jinping

LABARAI MASU NASABA

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

Babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban kasar Xi Jinping, ya isa birnin Hanoi, fadar mulkin kasar Vietnam ta jirgin sama na musamman a yau Talata bisa agogon wurin, inda ya fara ziyarar aiki a kasar bisa gayyatar da babban sakataren jam’iyyar kwaminis ta Vietnam Nguyen Phu Trong, da shugaban jamhuriyar gurguzu ta Vietnam Vo Van Thuong suka yi masa.

Yayin jawabin da Xi ya gabatar a filin jiragen sama na Hanoi, ya bayyana cewa, Vietnam muhimmiyar kasa ce a Asiya, kuma muhimmiyar mamba ce a kungiyar ASEAN. Ya ce a ’yan shekarun baya, bisa jagorancin jam’iyyar kwaminis ta Vietnam, jama’ar kasar Vietnam suna aiki tukuru don binciken hanyar ci gaba da ta dace da yanayin kasarsu, kuma ana inganta hanyar gyare-gyare a dukkan fannoni, kana tasirin kasar a cikin yankuna, har ma da duniya baki daya na ci gaba da karuwa.

Ya kara da cewa, kasashen Sin da Vietnam suna kusa da juna, an kuma kulla abokantakar gargajiya tsakaninsu tun da can. Kaza lika dangantakar dake tsakanin kasashen Sin da Vietnam da tsoffafin shugabannin kasashen biyu suka kafa wadda ta samu bunkasawa, arziki ne mai daraja na al’ummun kasashen biyu. Har ila yau, bangaren Sin yana daukar bunkasar dangantakar kasashen Sin da Vietnam a matsayin abu mai muhimmanci, yayin da Sin take kokarin raya dangantakar diplomassiya tare da kasashe makwabta.

ADVERTISEMENT
  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Sa Kaimi Ga Kare Hakkin Dan Adam

Xi Jinping ya kara da cewa, yana sa ran a yayin wannan ziyarar aiki, zai yi musayar ra’ayi tare da shugabannin kasar Vietnam, game da wasu abubuwa masu muhimmanci, da jagoranci, da batutuwa masu alaka da kasa da kasa, da na shiyya-shiyya, wadanda kasashen biyu suke damuwa da su, da kuma jam’iyyun siyasa na kasashen biyu, ta yadda za a kai dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu zuwa wani sabon mataki. (Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Next Post
ECOWAS Ta Shimfida Sabbin Ka’idoji Domin Janye Wa Nijar Takunkumi

ECOWAS Ta Shimfida Sabbin Ka'idoji Domin Janye Wa Nijar Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.