• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar Sabuwar Shekarar Gargajiya Ga Al’ummar Kasar Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar Sabuwar Shekarar Gargajiya Ga Al’ummar Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A madadin kwamitin kolin JKS da majalisar gudanarwar kasar, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika gaisuwar sabuwar shekarar gargajiya ta kasar ga al’ummar Sinawa yayin wata liyafar da aka yi yau Alhamis a birnin Beijing.

Shugaba Xi ya gabatar da jawabi a yayin liyafar wadda aka yi a dakin taron jama’a na birnin Beijing, inda ya mika gaisuwa ga Sinawa ‘yan kabilu daban daban da ‘yan uwa da ke Hong Kong da Macao da Taiwan da kuma Sinawa mazauna ketare.

  • Yadda Nijeriya Ta Taka Rawar Gani Har Zuwa Zagayen Karshe Na Gasar AFCON
  • Kusan Kaso 90 Na Wadanda Suka Amsa Wata Kuri’ar Ra’ayin Jama’a A Duniya, Sun Ce Rikici Tsakanin Bangarorin Amurka Na Neman Zama Jiki 

Shugaba Xi ya ce, cikin shekarar da ta gabata, kasar Sin ta nacewa akidar neman ci gaba yayin da take tabbatar da zaman karko da inganta farfadowar tattalin arziki.

Da yake lissafo ci gaban da aka samu, shugaba Xi ya ce yawan hatsin da ake samarwa ya kai sabon matsayin koli, kuma an samu manyan nasarori a bangaren kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha. Ya ce gyare-gyare da bude kofa sun ci gaba da zurfafa a kasar Sin, kana muhallin halittu ya ci gaba da kyautata, baya ga sabbin matakai da aka dauka na zamanantar da tsarin tsaron kasa da rundunonin sojin kasar.

Xi ya bayyana cewa, a shekarar 2024 za a cika shekaru 75 da kafa Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin, kuma shekarar tana da muhimmanci wajen cimma muradu da burikan dake cikin shirin raya kasa na shekaru 5-5 karo na 14, wato daga shekarar 2021 zuwa ta 2025.

Labarai Masu Nasaba

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

A cewarsa, Sinawa sun yi imanin cewa dabbar Loong, ko Dragon a Turance, alama ce ta karfi da rashin tsoro da kyautatawa. A don haka ya yi fatan a cikin shekarar Dragon dukkan Sinawa za su kara samun ci gaba cikin jajircewa da karsashi, da hada hannu wajen bude wani sabon babin ci gaba a yunkurin zamanantar da kasar.

A bana, ranar 10 ga watan ne za ta kasance ranar ta 1 ta sabuwar shekara bisa kalandar gargajiya ta kasar Sin. (Fa’iza Mustapha)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar ‘Yansanda Ta Shelanta Neman Dakta Idris Dutsen Tanshi Ruwa A Jallo

Next Post

Xi Jinping Da Putin Sun Zanta Ta Wayar Tarho

Related

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

17 minutes ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

2 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

3 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

5 hours ago
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157
Daga Birnin Sin

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

7 hours ago
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

1 day ago
Next Post
Xi Jinping Da Putin Sun Zanta Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Da Putin Sun Zanta Ta Wayar Tarho

LABARAI MASU NASABA

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.