Yau Lahadi 3 ga wata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya mika sakon taya Shehbaz Sharif murnar zama firaministan kasar Pakistan.
A sakon nasa, shugaba Xi ya ce, yana da yakinin cewa, a karkashin jagorancin firaministan gami da sabuwar gwamnatin Pakistan, tare kuma da hadin-gwiwa da kokarin bangarori daban-daban na kasar, babu shakka Pakistan za ta iya samun karin nasarori a sha’anin samar da ci gaban kasa.
Firaministan kasar Sin Li Qiang shi ma ya taya Shehbaz Sharif murna. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp