• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Kasar Guinea Bissau

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Kasar Guinea Bissau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da maraicen yau Laraba 10 ga watan nan ne, a babban dakin taron al’umma dake Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Guinea Bissau, Umaro Mokhtar Sissoco Embaló, wanda a yanzu haka yake ziyarar aiki a kasar, inda shugabannin biyu suka amince da daga matsayin dangantakarsu zuwa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.

A yayin shawarwarin, Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar Sin da Afirka dukkansu suna da wayewar kai mai burgewa, kuma dukkansu na dakon tarihin mulkin mallaka da mamaya da aka musu, kuma dukkansu na mutunta tare da tabbatar da ‘yancin kai da ‘yancin kasa. Kasar Sin da kasashen Afirka na taimakawa juna cikin gaskiya, kuma sun zama abin koyi na hadin gwiwar da ke tsakanin kasashe masu tasowa. Za a gudanar da sabon taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a Beijing a wannan kaka. Kasar Sin a shirye take ta yi hadin gwiwa tare da Guinea Bissau da sauran kasashen Afirka, domin tattaunawa kan tsare-tsaren hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a wannan sabon zamani, da kare moriyar kasashe masu tasowa, da daidaito da adalci tsakanin kasa da kasa, da yin hadin gwiwa don gina wata babbar al’umma mai makomar bai daya ga Sin da Afirka, da sa kaimi ga gina al’umma mai makomar bai daya ga bil Adama.

  • Fakewa Da Batun Kasar Sin Ba Zai Taimaka Wa NATO Cimma Burinta Da Ya Shafi Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba
  • Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Masu Bayyana Ra’ayoyi Suka Zargi Nuna Fin Karfi Da Amurka Ta Yi A Harkokin Intanet

A nasa bangare, Embaló ya ce, kasar Sin ba ta taba yin mulkin mallaka ba, ba ta taba tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wasu kasashe ba, ba ta taba yin katsalandan ga sauran kasashe ba, kuma tana girmama kananan kasashe da daidaito da mutuntawa. Kasar Sin ta kasance tana bin kalamanta da ayyuka. Abin da kasar Sin ta kawo wa kasashen Afirka shi ne makarantu, asibitoci, hanyoyi da sauran ayyukan hadin gwiwa da ke amfanar jama’ar Afirka. Kasar Guinea-Bissau ta yaba da muhimmiyar rawar da kasar Sin take takawa, da kyakkyawar gudummawar da take bayarwa wajen taimakawa ci gaban nahiyar Afirka, kuma tana goyon bayan kasar Sin sosai wajen karbar bakuncin sabon taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka.

Bayan tattaunawar, shugabannin kasashen biyu, tare suka rattaba hannu kan wasu takardu kan aiwatar da shirin raya kasa da kasa, da raya tattalin arziki, da binciken kwastam, da nazarin kasa da ma’adinai. (Yahaya)

 

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaKasuwanciSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Ya Yi Sabbin Naɗe-Naɗe 8

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Barawon Babura 6 A Sokoto

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

13 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

14 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

15 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

16 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

17 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

'Yansanda Sun Kama Barawon Babura 6 A Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.