• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Kasar Guinea Bissau

by Sulaiman and CGTN Hausa
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Kasar Guinea Bissau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da maraicen yau Laraba 10 ga watan nan ne, a babban dakin taron al’umma dake Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Guinea Bissau, Umaro Mokhtar Sissoco Embaló, wanda a yanzu haka yake ziyarar aiki a kasar, inda shugabannin biyu suka amince da daga matsayin dangantakarsu zuwa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.

A yayin shawarwarin, Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar Sin da Afirka dukkansu suna da wayewar kai mai burgewa, kuma dukkansu na dakon tarihin mulkin mallaka da mamaya da aka musu, kuma dukkansu na mutunta tare da tabbatar da ‘yancin kai da ‘yancin kasa. Kasar Sin da kasashen Afirka na taimakawa juna cikin gaskiya, kuma sun zama abin koyi na hadin gwiwar da ke tsakanin kasashe masu tasowa. Za a gudanar da sabon taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a Beijing a wannan kaka. Kasar Sin a shirye take ta yi hadin gwiwa tare da Guinea Bissau da sauran kasashen Afirka, domin tattaunawa kan tsare-tsaren hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a wannan sabon zamani, da kare moriyar kasashe masu tasowa, da daidaito da adalci tsakanin kasa da kasa, da yin hadin gwiwa don gina wata babbar al’umma mai makomar bai daya ga Sin da Afirka, da sa kaimi ga gina al’umma mai makomar bai daya ga bil Adama.

  • Fakewa Da Batun Kasar Sin Ba Zai Taimaka Wa NATO Cimma Burinta Da Ya Shafi Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba
  • Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Masu Bayyana Ra’ayoyi Suka Zargi Nuna Fin Karfi Da Amurka Ta Yi A Harkokin Intanet

A nasa bangare, Embaló ya ce, kasar Sin ba ta taba yin mulkin mallaka ba, ba ta taba tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wasu kasashe ba, ba ta taba yin katsalandan ga sauran kasashe ba, kuma tana girmama kananan kasashe da daidaito da mutuntawa. Kasar Sin ta kasance tana bin kalamanta da ayyuka. Abin da kasar Sin ta kawo wa kasashen Afirka shi ne makarantu, asibitoci, hanyoyi da sauran ayyukan hadin gwiwa da ke amfanar jama’ar Afirka. Kasar Guinea-Bissau ta yaba da muhimmiyar rawar da kasar Sin take takawa, da kyakkyawar gudummawar da take bayarwa wajen taimakawa ci gaban nahiyar Afirka, kuma tana goyon bayan kasar Sin sosai wajen karbar bakuncin sabon taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka.

Bayan tattaunawar, shugabannin kasashen biyu, tare suka rattaba hannu kan wasu takardu kan aiwatar da shirin raya kasa da kasa, da raya tattalin arziki, da binciken kwastam, da nazarin kasa da ma’adinai. (Yahaya)

 

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaKasuwanciSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Ya Yi Sabbin Naɗe-Naɗe 8

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Barawon Babura 6 A Sokoto

Related

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

21 hours ago
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara
Daga Birnin Sin

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

22 hours ago
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

1 day ago
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

1 day ago
Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

2 days ago
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025
Daga Birnin Sin

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

2 days ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

'Yansanda Sun Kama Barawon Babura 6 A Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.