• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Takwaransa Na Ukraine

by CMG Hausa
3 years ago
Xi Jinping

Bisa gayyatar da aka yi masa, da yammacin yau Laraba, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Ukraine Volodymyr Zelensky. Yayin zantawar ta su, shugabannin biyu, sun yi musayar ra’ayoyi game da alakar kasashen biyu da batun rikicin Ukraine.

A nasa tsokaci, Xi Jinping ya bayyana cewa, duk irin sauyin da aka samu a harkokin kasa da kasa, Sin a shirye take ta yi aiki tare da Ukraine, wajen ingiza hadin gwiwar cimma moriyar juna tsakanin kasashen 2.

  • Xi Jinping Ya Aike Da Wasika Ga Taron Kawancen Kare Al’adun Gado Na Asiya

Game da rikicin Ukraine kuwa, shugaba Xi ya ce kasar sa za ta ci gaba da goyon bayan wanzar da zaman lafiya, kuma muhimmin burin ta zai kasance bunkasa zaman lafiya, da ingiza komawa shawarwari.

Ya ce yana fatan dukkanin sassan da batun ya shafa za su yi nazari mai zurfi game da rikicin Ukraine, su kuma yi aiki tare ta hanyar tattaunawa, ta yadda za a kai ga hawa turbar wanzar da zaman lafiya, da daidaito na tsawon lokaci a yankunan Turai.

Bugu da kari, shugaban na Sin ya ce gwamnatin sa za ta aike da wakilin musamman game da batutuwan Turai da Asiya, domin ya ziyarci Ukraine, da sauran wasu kasashem yankin, ta yadda za a kai ga zurfafa zantawa da dukkanin sassa, game da matakan shawo kan rikicin Ukraine ta hanyar siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Kaza lika, Sin za ta samar da rukunonin tallafin jin kai ga Ukraine, kuma a shirye take da ta ci gaba da ba da duk wani taimako ga kasar gwargwadon karfin ta.

A nasa bangare kuwa, shugaba Zelensky, ya ce Sin na nacewa ka’idoji da dokokin MDD, a fannin harkokin kasa da kasa, tana kuma taka rawar gani a harkokin kasa da kasa. Ya ce Ukraine na godiya bisa tallafin jin kai da Sin din ke samar mata, tana kuma maraba da muhimmiyar rawa da Sin din ke takawa bangaren dawo da zaman lafiya, da warware rikicin kasar ta hanyar diflomasiyya. (Mai fassarawa: Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Next Post
Shugaba Buhari Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarorin Gwamnati 6

Shugaba Buhari Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarorin Gwamnati 6

LABARAI MASU NASABA

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.