A yammacin yau 16 ga watan Afrilun nan ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan kasar Malaysia Anwar Ibrahim a fadar mulkin firaminstan na Malaysia.
Xi Jinping ya ce a shirye yake ya yi aiki tare da Anwar wajen habaka ci gaban al’ummar Sin da Malaysia mai kyakkyawar makomar bai daya bisa manyan tsare-tsare kuma a babban mataki, da kara ba da gudummawa wajen samun wadata da kwanciyar hankali a yankin. Ya kuma bukaci a yi kokari tare wajen yin watsi da matakan raba gari, da kawo cikas ga tsarin samar da kayayyaki ta hanyar bude kofa, da hadin gwiwa.
A nasa bangaren kuwa, Anwar cewa ya yi, a yayin da ake fuskantar karuwar daukar matakai bisa ra’ayin bangare daya, kasar Malaysia a shirye take ta karfafa hadin gwiwa da kasar Sin domin tinkarar kasada da kalubale tare. Kana, kungiyar ASEAN ba za ta amince da duk wani harajin da aka sanya bisa radin kai ba, kuma za ta kiyaye bunkasar tattalin arziki ta hanyar hadin gwiwa da dogaro da kai tare.
A wannan rana har ila yau, Xi Jinping da Anwar sun halarci bikin musayar takardun hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp