• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 month ago
Xi

A yau Alhamis 4 ga wannan wata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da na kasar jamhuriyar Kongo Denis Sassou Nguesso wadanda suka zo kasar Sin domin halartar bikin murnar cika shekaru 80 da cimma nasarar yakin kin mamayar dakarun Japan, da yakin kin tafarkin murdiyya na duniya a babban dakin taron Beijing, fadar mulkin kasar.

Yayin ganawar, shugaba Xi da takwaransa na Zimbabwe sun sanar da cewa, za su daga alakar kasashensu zuwa ta samar da kyakkyawar makomar bil Adam ta bai daya a ko da yaushe, inda Xi ya nuna cewa, bana ake cika shekaru 45 da kafuwar huldar diplomasiya tsakanin Sin da Zimbabwe, don haka ya dace kasashen biyu su kara karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, musamman ma a bangarorin gina manyan ababen more rayuwar jama’a, da hakar ma’adinai, da zuba jari, da gudanar da cinikayya.

A nasa bangare kuwa, shugaba Mnangagwa ya bayyana cewa, kasar Sin ta gabatar da shawarwari da dama, kuma tana taka rawar gani a harkokin kasa da kasa, don haka bangaren Zimbabwe ke fatan yin kokari tare da na Sin wajen kiyaye adalci a fadin duniya.

Yayin ganawa da takwaransa na jamhuriyar Kongo kuwa, Xi ya yi nuni da cewa, huldar dake tsakanin Sin da jamhuriyar Kongo ta zama misali na sada zumunta tsakanin Sin da Afirka. Kazalika, ana sa ran za a bude wani sabon shafi na hadin gwiwar cinikayya da zuba jari tsakanin kasashen biyu.

A nasa tsokaci kuwa shugaba Sassou, cewa ya yi kasar Sin ta shirya bikin murnar cika shekaru 80 da cimma nasarar yakin kin mamayar dakarun Japan, da yakin kin tafarkin murdiyya na duniya cikin nasara, lamarin da ya nuna aniyar hadin kai ta al’ummun kasar Sin ga duniya. Yana kuma fatan kara azama tare da kasar Sin wajen kare zaman lafiya a fadin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

Har ila yau, a dai yau din shugaba Xi ya gana da babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar juyin juya halin jama’ar kasar Laos kuma shugaban kasar Thongloun Sisoulith, da shugaban kasar Vietnam Luong Cuong, da shugaban kasar Cuba Miguel Diaz-Canel, da firayin ministan jamhuriyar Slovakia Robert Fico, da shugaban kasar Serbia Aleksandar Vucic a nan birnin Beijing. (Mai fassara: Jamila)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki
Daga Birnin Sin

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Next Post
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.