• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi: Ya Kamata A Hada Hannu Domin Tafiyar Da Tattalin Arzikin Duniya Bisa Adalci Da Daidaito

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Xi

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a inganta yanayin tafiyar da tattalin arzikin duniya da gina shi ta hanyar hadin gwiwa. 

 

Xi Jinping ya bayyana haka ne cikin muhimmin jawabin da ya gabatar mai taken “Hada Hannu Domin Tafiyar da Tsarin Tattalin Arzikin Duniya Bisa Adalci da Daidaito,” yayin zama na II na taron kungiyar G20 karo na 19, a jiya Litinin.

  • Kamata Ya Yi Sin Da Amurka Su Mai Da Hankalinsu A Kan Ci Gaban Duniya
  • An Kashe Mutum 50, An Sace 170 Cikin Wata 7 A Kaduna

A cewarsa, a matsayinsu na manyan masu bayar da rance, ya kamata cibiyoyin kudi na kasa da kasa da kamfanoni da daidaikun ‘yan kasuwa masu bayar da bashi, su shiga cikin shirin rage yawan basussuka da tsawaita lokacin biya, ga kasashe masu tasowa.

 

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Ya kuma yi kira da a inganta tsarin tafiyar da harkokin kudi na duniya da gina tattalin arzikin duniya mai karko. Yana cewa, akwai bukatar hada hannu domin tabbatar da daidaiton tsarin kasuwar hada hadar kudi na duniya da kare yaduwar sauye-sauye manufofin kudi na cikin gida zuwa sauran yankuna. Haka kuma, ya kamata kasashe masu wadata su sauke nauyin dake wuyansu a wannan bangare.

 

Har ila yau, shugaba Xi Jinping ya yi kira da a gina tattalin arzikin duniya mai bude kofa, yana cewa, “ya kamata mu ingiza yi wa hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO) garambawul, da adawa da kariyar cinikayya da ra’ayin bangare daya, da dawo da tsarin warware takkadama mai inganci nan bada jimawa ba, da sanya yarjejeniyar saukaka zuba jari domin samun ci gaba, cikin tsarin dokokin WTO da kuma cimma matsaya daya kan yarjejeniyar cinikayayya ta intanet.

 

Ya kuma yi kira da a inganta tsarin tafiyar da harkokin dijital da gina tattalin arziki dake mayar da hankali ga kirkire-kirkire. Ya ce akwai bukatar inganta tsarin jagoranci da hadin gwiwa a bangaren kirkirarriyar basira wato AI, domin tabbatar da kowa ya amfana da fasahar ta AI, ba kawai kasashe da mutane masu wadata ba.

 

Bugu da kari, ya yi kira da a kyautata yanayin kula da muhallin duniya da gina tsarin tattalin arziki mai dacewa da kare muhalli. Ya ce “sauyawa zuwa amfani da makamashi mai tsafta da wadatar makamashin, babban batun ne. Don haka ya kamata mu yi amfani da dabarar nan ta karfafa sabon, kafin kawar da tsoho,’ tare da maye gurbin tsohon makamashin da sabo, ta hanya mai tsari da dorewa.” (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Next Post
Gwamna Biodun Ya Amince Da ₦70,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Ekiti

Gwamna Biodun Ya Amince Da ₦70,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Ekiti

LABARAI MASU NASABA

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.