A yau Juma’a, rundunar sojin kasar Sin wato rundunar ‘yantar da al’ummar kasar ta (PLA), ta kaddamar da wata rundunar samar da bayanai.
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ne ya mika tuta ga rundunar, yayin bikin kafa ta da ya gudana yau, a birnin Beijing.
Xi Jinping wanda shi ne sakatare janar na kwamitin kolin JKS kuma shugaban hukumar sojin kasar, ya nanata bukatar yin kokarin gaske wajen gina rundunar samar da bayanai mai karfi, wadda ta dace da zamani. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp