• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Dace Sin Da Afirka Su Bunkasa Hadin Gwiwar Cin Gajiya Daga Fasahohin Amfani Da Makamashi Maras Illa Ga Muhalli

by CMG Hausa
3 years ago
Afirka

Yayin da hankulan duniya ke kara karkata ga yadda za ta karke a taron COP27, na bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD, masharhanta da dama na ganin taron babbar dama ce ga daukacin masu ruwa da tsaki, ta su hada karfi da karfe wajen lalubo dabarun gaggauwa na shawo kan kalubalen sauyin yanayi, ciki kuwa har da dabarun rage radadin sauyin yanayin, da gano fasahohin jurewa da dorewar rayuwa tare da kalubalen, da rage asarar da sauyin yanayin ka iya haifarwa, da ma batun samar da kudaden gudanar da wadannan ayyuka.

Tuni dai aka yi imanin cewa, nahiyar Afirka na cikin yankunan duniya dake fitar da mafi karancin sinadarai, da iska mai gurbata muhalli a duniya, amma a hannu guda, nahiyar na sahun gaba wajen dandana kuda daga mummunan tasirin sauyin yanayi.

  • CMG Ya Shirya Bikin Musammam Game Da “Sabon Tafarki Na Sin Da Duniya” A Afirka

Masharhanta na ganin duba da yadda kasar Sin ke kan gaba, wajen cin gajiya daga fasahohin dakile sauyin yanayi, musamman fannin bunkasa amfani da nauoin makamashi marasa gurbata muhalli, da wadanda ake iya sabuntawa. Kuma kasar ta jima da kasancewa abokiyar tafiya ga kasashen Afirka a dukkanin fannonin ci gaba, yanzu lokaci yayi da kasashen na Afirka za su fadada koyi daga kasar Sin a wannan fanni.

A cewar Frederick Mutesa, wani kwararre a fannin ilimin samar da ci gaba dan kasar Zambia, kasar Sin ta nunawa duniya kwazon ta a fili wajen bunkasa ci gaba mai dorewa, da raya manufofi na dakile kalubale da matsalolin da sauyin yanayi ke haifarwa. Don haka lokaci ya yi da kasashen Afirka za su gaggauta yin hadin gwiwa da Sin, ta yadda za su yi koyi, da kuma cin gajiyar kwarewar Sin a wannan fanni.

Ko shakka ba bu wannan shawara ce mai kyau, domin kuwa akasarin kasashen nahiyar Afirka na da albarkatu musamman na hasken rana, yayin da a daya bangaren kasar Sin ke da kwarewa, da fasahohin bunkasa samar da makamashi ta hasken rana, wanda hakan ke nuna cewa, idan har sassan biyu sun yi hadin gwiwa, tabbas za a ci babbar gajiya daga makamashi maras gurbata muhalli.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

Baya ga fannin raba fasahohi da kasashen Afirka, fannin samar da kudaden dakile tasirin sauyin yanayi, shi ma muhimmin bangare ne da kasashen Afirka za su iya cin gajiya daga Sin, kasancewar dama akwai kyakkyawar dangantaka, da cudanya tsakanin kasashen Afirka da Sin karkashin dandalin FOCAC na bunkasa hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da kuma irin tallafi na samar da manyan ababen more rayuwa da kasashen Afirka ke samu daga Sin, karkashin manufofin samar da ci gaba na shawarar ziri daya da hanya daya.

Duk wadannan dalilai, na kara nuna muhimmancin aza kyakkyawan mafari, na ingiza hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka a fannin kare muhalli, da bunkasa cin gajiya daga nauoin makamashi da ake iya sabuntawa.(Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
Daga Birnin Sin

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Next Post
Hedikwatar Tsaro Ta Ayyana Neman ‘Yan Ta’adda 19 Ruwa A Jallo, Ta Sa Ladar Miliyan 5 Kan Kowanne

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta’adda 29 Da Cafke Masu Taimaka Musu 10 Da Naira Miliyan 15

LABARAI MASU NASABA

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legas

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.