• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasashen Larabawa Su Dauki Darasi Daga Kasar Sin, Su Daina Biyewa Kasashen Yamma

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Kasashen Larabawa Su Dauki Darasi Daga Kasar Sin, Su Daina Biyewa Kasashen Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahoton Arab Barometer da kafar yada labarai ta BBC ta wallafa a baya bayan nan, ya ce kasashen Larabawa sun yanke kauna da tsarin demokuradiyyar kasashen yammacin duniya, saboda yadda tattalin arzikinsu ya yi rauni a karkashin tsarin.

Wannan rahoto ya tuna min da ziyarar da shugaban Amurka zai kai yankin gabas ta tsakiya a cikin wannan mako, wadda ya bayyana a matsayin mai muhimmanci ga tsaron kasarsa da kuma neman nasara a takararta da Sin.

  • Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dauki Jerinta Da Muhimmanci

Amurka ta gaza gane cewa, kan al’umma ya waye, babu wanda ke bukatar danniya da fifiko irin nata da kuma katsaladan da take yi cikin harkokin da ba su shafe ta ba. Kasashen sun ba ta dama, kuma sun ga aikin hannunta, sun ga yadda ta ingiza yake-yake ko ma kaddamar da yake-yake da tashin hankali a yankin.

Don haka, dukkan kasashe masu tasowa sun fahimci cewa, Amurka ita kanta kadai ta sani, ba ta damu da sauran kasashe ba.

A daya bangaren, a matsayinta na kasa mai tasowa, an ga yadda kasar Sin ke kiyaye cikakken ’yancin kasa da kasa da martabawa da mutunta su.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

An ga kuma irin jajircewarta wajen kyautata dangantakar moriyar juna da hadin gwiwar kasa da kasa. Kana ta zama misali na kasar da ta samu ci gaba na a zo a gani, bisa dabarun da ta dauka bisa la’akari da yanayinta, ba wai koyi da wata kasar yamma ba. Don haka, kasar Sin ta zama abun koyi a fannin tsarin demokradiyya da ci gaba.

Abun da ya kamata kasashen gabas ta tsakiyar su yi a yanzu shi ne, daukar darasi daga Sin, su tsara yanayin demokradiyyarsu ta hanyar da ta dace da muradu da moriyar al’ummominsu domin samun ci gaban da suke muradi.

Su kadai suke san yanayin da suke ciki da abun da ya fi dacewa da su, don haka su kadai ne za su iya magance matsalolinsu ba wai biyewa Amurka da kawayenta ba.

Ita kuma Amurka, kamata ya yi ta fahimci cewa, ba takara ya kamata ta yi da Sin ba, domin ba za ta ci nasara ba. Abun da ya kamata ta yi shi ne, hada hannu da kasar Sin a matsayinsu na manyan kasashe, domin samun moriyar juna da tallafawa tabbatar zaman lafiya a duniya da bunkasa tattalin arzikinta da gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a duniya. (Fa’iza Muhammad Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Tambuwal Ya Yi Ta’aziya Ga Bagudu Da Malami Bisa Hadarin Mota Da Ya Ci Rayuka A Kebbi

Next Post

Kalubalen Rashin Tsaro: Ba Za Mu Kara Cewa Buhari Uffan Ba – ACF

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

45 minutes ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

2 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

3 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

4 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

5 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

7 hours ago
Next Post
Kalubalen Rashin Tsaro: Ba Za Mu Kara Cewa Buhari Uffan Ba – ACF

Kalubalen Rashin Tsaro: Ba Za Mu Kara Cewa Buhari Uffan Ba – ACF

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.