• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauke Nauyin Dake Wuyan Ta Game Da Kasar Afghanistan

by Sulaiman and CGTN Hausa
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauke Nauyin Dake Wuyan Ta Game Da Kasar Afghanistan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan ba a manta ba a karshen watan Agustan shekarar 2021 ne dakarun sojin Amurka suka fice daga kasar Afghanistan, bayan shafe shekaru 20 suna yaki a kasar, matakin da ya daidaita kasar tare da barin al’ummun ta cikin mawuyacin hali.

Masharhanta da dama na cewa har gobe, Amurka ba ta sauke nauyin dake wuyanta na tallafawa wajen sake farfado da Afghanistan ba, kuma hakan ya yi daidai da ra’ayin sassan kasa da kasa da suka halarci taro karo na 3 da MDD ta kira game da Afghanistan a birnin Doha na kasar Qatar.

  • JAMB Ta Bankaɗo Ɗalibai 3000 Da Suka Kammala Karatun Bogi
  • Xi Jinping Ya Gana Da Vladimir Putin

Ko shakka babu, Amurka ba za ta iya sauya halin kunci da ta jefa Afghanistan a ciki ba, duba da irin ta’annatin da ya wakana cikin wadancan shekaru 20, inda yakin da Amurka ta jagoranta ya haifar da kisan ’yan kasar har 174,000, ciki har da fararen hula sama da 30,000, tare da raba kusan kaso daya bisa uku na daukacin al’ummar kasar da matsugunnansu.

Baya ga ainihin abubuwan da suka auku yayin yakin da Amurka ta yi ikirarin ta yi da kungiyar Taliban, yakin ya bar wa Afghanistan kusan kaso 20 bisa dari, na bama-bamai da ba su tashi ba, wadanda ake da matukar bukatar kawar da su, yayin da a lokuta daban daban su kan tashi su hallaka karin fararen hula.

Kazalika, ya zuwa shekarar nan ta 2024, yakin da Amurka ta yi a Afghanistan ya jefa al’ummar kasar da yawansu ya kai kusan miliyan 23.7, adadin da ya haura rabin daukacin ’yan kasar cikin halin bukatar jin kai. Rahotanni sun tabbatar da cewa, a shekarar bana, ana bukatar kashe kudi har dala biliyan 3.06, don tallafawa al’ummun Afghanistan mabukata, wadanda yawansu ya kai miliyan 17.3, ko da yake har zuwa watan Mayun da ya shude, kaso 16.2 bisa dari ne kacal na kudaden aka iya samu domin gudanar da ayyukan.

Labarai Masu Nasaba

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Tabbas yakin Afghanistan ya dada tabbatar da cewa, tashin hankali ba ya warware wata matsala, illa dai kara ta’azzara halin matsi, da jefa fararen hula cikin halin kunci. Kuma mai yiwuwa tasirinsa ya wanzu zuwa tsawon shekaru masu yawa. Amma yanzu lokaci ne da ya dace Amurka ta saurari muryoyin sassan kasa da kasa, ta sauke nauyin dake wuyanta, na farfado da Afghanistan, ta hanyar kawar mata da takunkumai, da tallafawa wanzar da daidaito, zaman lafiya da ci gaban kasar.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfghanistanAmurkaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalar ‘Yan sandan Amurka Ta Nuna Karfin Tuwo Na Kara Tsananta

Next Post

Huldar Abotar Dindindin Tsakanin Sin Da Kazakhstan Na Samun Ci Gaba Zuwa Sabon Mataki

Related

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

29 minutes ago
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

2 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

20 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

20 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

22 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

23 hours ago
Next Post
Huldar Abotar Dindindin Tsakanin Sin Da Kazakhstan Na Samun Ci Gaba Zuwa Sabon Mataki

Huldar Abotar Dindindin Tsakanin Sin Da Kazakhstan Na Samun Ci Gaba Zuwa Sabon Mataki

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.