ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauke Nauyin Dake Wuyan Ta Game Da Kasar Afghanistan

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Amurka

Idan ba a manta ba a karshen watan Agustan shekarar 2021 ne dakarun sojin Amurka suka fice daga kasar Afghanistan, bayan shafe shekaru 20 suna yaki a kasar, matakin da ya daidaita kasar tare da barin al’ummun ta cikin mawuyacin hali.

Masharhanta da dama na cewa har gobe, Amurka ba ta sauke nauyin dake wuyanta na tallafawa wajen sake farfado da Afghanistan ba, kuma hakan ya yi daidai da ra’ayin sassan kasa da kasa da suka halarci taro karo na 3 da MDD ta kira game da Afghanistan a birnin Doha na kasar Qatar.

  • JAMB Ta Bankaɗo Ɗalibai 3000 Da Suka Kammala Karatun Bogi
  • Xi Jinping Ya Gana Da Vladimir Putin

Ko shakka babu, Amurka ba za ta iya sauya halin kunci da ta jefa Afghanistan a ciki ba, duba da irin ta’annatin da ya wakana cikin wadancan shekaru 20, inda yakin da Amurka ta jagoranta ya haifar da kisan ’yan kasar har 174,000, ciki har da fararen hula sama da 30,000, tare da raba kusan kaso daya bisa uku na daukacin al’ummar kasar da matsugunnansu.

ADVERTISEMENT

Baya ga ainihin abubuwan da suka auku yayin yakin da Amurka ta yi ikirarin ta yi da kungiyar Taliban, yakin ya bar wa Afghanistan kusan kaso 20 bisa dari, na bama-bamai da ba su tashi ba, wadanda ake da matukar bukatar kawar da su, yayin da a lokuta daban daban su kan tashi su hallaka karin fararen hula.

Kazalika, ya zuwa shekarar nan ta 2024, yakin da Amurka ta yi a Afghanistan ya jefa al’ummar kasar da yawansu ya kai kusan miliyan 23.7, adadin da ya haura rabin daukacin ’yan kasar cikin halin bukatar jin kai. Rahotanni sun tabbatar da cewa, a shekarar bana, ana bukatar kashe kudi har dala biliyan 3.06, don tallafawa al’ummun Afghanistan mabukata, wadanda yawansu ya kai miliyan 17.3, ko da yake har zuwa watan Mayun da ya shude, kaso 16.2 bisa dari ne kacal na kudaden aka iya samu domin gudanar da ayyukan.

LABARAI MASU NASABA

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Tabbas yakin Afghanistan ya dada tabbatar da cewa, tashin hankali ba ya warware wata matsala, illa dai kara ta’azzara halin matsi, da jefa fararen hula cikin halin kunci. Kuma mai yiwuwa tasirinsa ya wanzu zuwa tsawon shekaru masu yawa. Amma yanzu lokaci ne da ya dace Amurka ta saurari muryoyin sassan kasa da kasa, ta sauke nauyin dake wuyanta, na farfado da Afghanistan, ta hanyar kawar mata da takunkumai, da tallafawa wanzar da daidaito, zaman lafiya da ci gaban kasar.(Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95
Daga Birnin Sin

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
Next Post
Huldar Abotar Dindindin Tsakanin Sin Da Kazakhstan Na Samun Ci Gaba Zuwa Sabon Mataki

Huldar Abotar Dindindin Tsakanin Sin Da Kazakhstan Na Samun Ci Gaba Zuwa Sabon Mataki

LABARAI MASU NASABA

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.