• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Bikin Ranar Hausa Ta Duniya A Kano

by Salim Sani Shehu and Sulaiman
2 months ago
Ranar hausa

A ranar 26 ga watan Agustan 2023, kungiyar Zauren Hausa ta Nijeriya ta jagoranci gudanar da taron Ranar Hausa ta Duniya a Jihar Kano. Taron ya gudana ne a zauren taro na Hassan da ke cikin Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a (CAS), da ke Jihar Kano.

 

Taron, wanda ya gudana karkashin jagorancin Farfesa Maryam Mansur Yola, mataimakiyar shugabar Kungiyar Zauren Hausa ta Kasa, ya tabo abubuwa da dama da suka shafi rayuwar Bahaushe da al’adunsa da kuma yanayin yadda yake a da da yanzu.

  • An Bude Bikin Nune-Nune Na Masana’antar Manyan Bayanai Ta Big Data A Kudu Maso Yammacin Sin
  • Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Kafin a fara gudanar da taron, Malam Abdullahi Baba Dantse ya gabatar da wasannin zaurance ga mahalarta taron, sannan ya kara bayani kan muhimmancin zaurance a harshen Hausa.

 

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Yana mai cewa: “Da yawa yanzu an manta zaurance ko ba a yi, saboda yanayin yadda zamani yake. Amma a da, musamman ma idan ka je wajen da ka ga sun iya Hausa kuma su ba Hausawa ba ne, za ka iya juya harshe ta amfani da zaurance wajen canza yaren ba tare da wanda ka ke tare da shi ya fahimci me kake faa ba.”

 

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a (CAS), Dakta Sunusi Yakubu Ahmed, ya bayyana jin dadinsa matuka bisa zabar kwalejin don gudanar da wannan taron.

 

Dakta Sunusi ya ce: “Tun lokacin da na ga an yi irin wannan taron a Jami’ar Northwest, na bukaci nima ina da burin ace an kawo irin wannan taron wannan kwalejin. Kuma masu shirya wannan taron sun aminta tare da kawo wannan taron nan.”

 

Dakta Sunusi ya kara da cewa, Hausa harshe ne wanda ya bunkasa matukar gaske ta hanyar da ya yi nisan da ba za a iya cewa ga inda harshen ya tsaya ba.

 

Ya ci gaba da cewa ire-iren wadannan tarukan ne ke kara fito da muhimmancin harshen a idon duniya, da kuma ga wadanda suke ganin kamar harshen ba shi da amfani.

 

Ita kuwa Farfesa Maryam Mansur Yola jaddada muhimmancin wannan rana ta yi ga duk wani mai amfani da harshen Hausa.

 

Farfesa ta ce kamar yadda aka fara bikin jiya ta hanyar bayar da horo ga wadanda suke amfani da harshen musamman a ayyukansu, kamar ‘yan jarida da masu fassara da malaman makaranta, yau kuma za a gudanar da wassanni da kuma nuna wasu daga cikin al’adun Bahaushe.

 

Farfesa Maryam ta bayyana dalilin da ya sa aka zabi wannan rana don mayar da ita Ranar Hausa ta Duniya, sakamakon ranar ce da aka kirkiri haruffa masu lankwasa da suka hada da ‘d, ‘b, ‘k, da sauransu, wadanda ke matukar dada wa harshen armashi.

 

Daga cikin wadanda suka gabatar da jawabi a wajen taron, akwai Hon. Sulaiman Mukhtar Ishak, dan Majalisar Jiha mai wakiltar Karamar Hukumar Madobi, wanda kuma shi ne Shugaban Kwamitin Kula da Ilimi na Majalisar Dokoki ta Jihar Kano. Ya jaddada tare da nuna muhimmancin wannan harshe.

 

Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai Alhaji Sama’ila Ammani Mai Zare da Alhaji Garba Gasash, da Shugabannin Sashen Koyar da Harshen Hausa na manyan makarantun gaba da sikandire na Jihar Kano, da dalibai da malamai daga ciki da wajen jihar.

 

Masu wake-wake da makada sun nishadantar da mahalarta taron tare da baje basirar da Allah ya ba su ta hanyar amfani da harshen don isar da sako ko kuma bunkasa harshen.

 

Daga karshen taron an gudanar da wasannin dambe da langa da kuma nuna wasu daga cikin sana’o’in da Malam Bahaushe ke alfahari da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.