• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

by Sani Anwar
6 hours ago
in Labarai
0
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ko shakka babu, tsarin tantance lafiya kafin a kai ga yin aure, yana da matuƙar amfani a tsanin al’umma.

Ya kamata a lura da cewa, idan aka gano guda daga cikin masu shirin yin aure yana ɗauke da wannan cuta, ba fa auren ake fasa yi ba, illa kawai dai za a ɗora shi a kan magani ne na tsawon wani lokaci, sannan kuma da zarar ya warke daga wannan ciwo na hanta, sai a ɗaura auren.

Daga cikin dalilan saukar da shari’a, akwai batun kiyaye lafiya. Saboda da haka, wannan tsari na tantance lafiya kafin aure; ya kamata ya zama wajibi a kan kowa da kowa.

dan guda daga cikin ma’aurata yana ɗauke da wannan cuta ta hanta, zai iya harbin aboki ko abokiyar zaman tasa; ba tare da ya sani ba, wannan shi ita ce babbar hikimar yin gwaje-gwaje a tsakanin masu shirin yin aure, kafin su kai ga yi.

  • Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati
  • Yadda Ake Hada Miyar Hanta

Don haka, hanyoyin da ciwon hanta ke yaɗuwa sun haɗa da:

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

1- Musayar yawu ta hanyar sumbatar juna- Ma’ana, ta hanyar sumbatar juna a tsakanin ma’aurata, idan guda daga cikinsu na ɗauke da cutar, nan da nan ɗayan shi ma zai kamu da cutar.

2- Gaurayewar jini ko haɗuwar jini- Haɗuwar jini, misali; idan wani ya yi amfani da reza ya yanke, ɗayan ya yi amfani da ita, zai iya kamuwa da cutar, ko kuma wani abu maikama da haka.

3- Ɓangaren saduwa a tsakanin ma’aurata- A wajen saduwa tsakanin mata da miji, ta hanyar haɗuwa maniyyi ko maziyyi da sauran makamantansu, wannan cuta za ta samu hanyar shigewa nan take da ɗaya daga cikinsu na ɗauke da ita.

Don haka, waɗannan hanyoyi da aka ambata dukkanninsu na iya faruwa a zamantakewar aure, kamar yadda masana kiwon lafiya suka sanar.

Saboda haka, ya zama wajibi mutane su kiyaye tare da bin ƙa’idojin waɗannan masana, musamman ta fuskar aiwatar da gwaje-gwaje, kafin a kai ga yin aure.

Wajibi ne ka kiyaye tare da kula da lafiyarka da kuma ta iyalinka, domin kuma sai an tambaye ka a kan yadda ka kula da ita. Sannan, yin wannan gwaji ba wani kayan gabas ba ne, duk da cewa; wasu na nuna tsoronsu a fili wajen zuwa a gwada su, wai a cewarsu; suna zaman-zamansu ka da ce; ba su da lafiya.

A nan, irin abin da Bahaushe yake cewa ne, “An gudu, ba a tsira ba”. Don haka, tun wuri kafin ku kai ga yin aure, ku je kai da yarinyar da za ka aura a gwada ku, a tabbatar da kwa ɗauke da wannan cuta ta hanta.

Haka nan kuma, su ma sauran ma’aurata; da zarar guda daga cikinsu, ya ji alamu ko an tabbatar masa da yana ɗauke da wannan cuta, ya yi ƙoƙarin taimaka wa abokin zaman nasa, ta hanyar zuwa yin gwaje-gwaje da kuma yin rigakafin kamuwa da cutar.

Mutane da dama, ba su san cewa; ana yin rigakafin wannan cuta ba, wanda abu ne da aka jima ana yi; ba lallai sai wanda ya kamu da cutar ba, kowa ma zai iya zuwa a yi masa kamar yadda masu iya magana ke cewa; “Rigakafi ya fi maganai”. 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hanta
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

Next Post

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

9 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

9 hours ago
Hanta
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

11 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

13 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

13 hours ago
Hanta
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

16 hours ago
Next Post
Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Hanta

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.