• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Fadada Bude Kofar Kasar Sin Ke Haifar Da Damammaki Ga Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Fadada Bude Kofar Kasar Sin Ke Haifar Da Damammaki Ga Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai biyiyar manufofin kasar Sin na samar da ci gaba, ba zai gaza sanin shirin kasar na daidaita harkokin zuba jarin waje na shekarar nan ta 2025 da aka fitar ba, wanda ke kunshe da manufofi 20 da aka kasa cikin muhimman fannoni 4, wadanda suka hada da fadada bude kofa bisa radin kai, da kyautata damammakin zuba jari, da daga matsayin dandalolin bude sassan tattalin arziki, da kara inganta tsarin samar da hidimomi masu nasaba.

Masharhanta da dama na kallo wannan shiri a matsayin manuniya, dake kara tabbatar da burin kasar Sin na dada bude kofofinta ga sassan kasa da kasa.

  • Sojoji Sun Kashe Ƙwararren Mai Haɗa Wa Boko Haram Bam A Borno
  • Sin Za Ta Kara Ingiza Samar Da Kudaden Gudanar Da Kamfanoni Masu Zaman Kansu

Kamar dai yadda muka sani, batun bude kofa na kan gaba cikin manufofin kasar Sin na samar da ci gaban kasa, kana hakan daya ne daga ginshikan zamanantarwa irin ta Sin. Kazalika, turba ce ta samar da wadata, da bude sabbin babuka na cimma nasarar zamanantarwa irin ta Sin.

Karkashin hakan, kasar Sin ta shafe sama da shekaru 40 tana ta aiwatar da managartan matakai, kama daga bude yankunan musamman na raya tattalin arziki, zuwa bude yankunan gwaji na gudanar da cinikayya maras shinge, da aiwatar da shawarar nan ta “ziri daya da hanya daya” ko BRI. Dukkanin wadannan matakai ana daidaita su ne da dunkulallen tsarin raya tattalin arzikin duniya, tare da fitar da sabon salon hadin gwiwar kasa da kasa.

Zuwa yanzu, kasar Sin ta himmatu wajen aiwatar da manufofin kara bude kofofinta, ta kuma cimma manyan nasarori sakamakon aiwatar da sauye-sauye. Har ila yau, tana ta aiwatar da matakan zurfafa bude kofa a karin sassan samar da ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Yayin da tattalin arzikin kasar Sin ke kara samun tagomashi, masana daga sassa daban daban, na ganin hakan dama ce ta ci gaban duniya baki daya. Kamar dai yadda sakamakon wani bincike, na asusun ba da lamuni na duniya IMF ya nuna yadda bunkasar tattalin arzikin kasar Sin ke shafar ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya. Binciken ya nuna bunkasar tattalin arzikin Sin da karin kaso daya bisa dari, yake haifar da matsakaicin bunkasar tattalin arzikin sauran sassan kasa da kasa da kaso 0.3 bisa dari.

Duba da haka, ma iya cewa duniya za ta ci gaba da shan romon bunkasar tattalin arzikin kasar Sin, yayin da kasar ke ta kara fadada manufofinta na bude kofa ga sassan duniya. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Sanata Natasha Na tsawon Watanni 6 Saboda Rashin Da’a

Next Post

Shugaban NAN:Muna Iya Ganin Basirar Sin Ta Manyan Taruka Biyu Da Take Gudanarwa Yanzu

Related

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya
Daga Birnin Sin

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

13 hours ago
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

14 hours ago
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi
Daga Birnin Sin

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

17 hours ago
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

17 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

19 hours ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

19 hours ago
Next Post
Shugaban NAN:Muna Iya Ganin Basirar Sin Ta Manyan Taruka Biyu Da Take Gudanarwa Yanzu

Shugaban NAN:Muna Iya Ganin Basirar Sin Ta Manyan Taruka Biyu Da Take Gudanarwa Yanzu

LABARAI MASU NASABA

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

August 28, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

August 28, 2025
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

August 28, 2025
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

August 28, 2025
Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

August 27, 2025
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

August 27, 2025
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 27, 2025
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.