• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Hada Hannun Kasa Da Kasa Wajen Inganta Muhallin Duniyarmu Ta Bai Daya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Kasar Sin Ke Hada Hannun Kasa Da Kasa Wajen Inganta Muhallin Duniyarmu Ta Bai Daya

default

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya, kamfanin samar da motoci na kasar Sin da aka san shi da BYD, ya samar da mota mai aiki da lantarki ta miliyan 5, kuma hakan ya faru ne kasa da shekara guda daga lokacin da ta samar da nau’in motar ta miliyan 3. A watan Yulin da ya gabata kuma, an samar da mota mai aiki da wutar lantarki ta miliyan 20 a kasar ta Sin. 

Lallai bisa ga jagorancin gwamnatin kasar da ma tallafi da ta samar, kasar ta Sin ta samu gaggarumin ci gaba ta fannin samar da motoci masu aiki da lantarki, haka kuma ta zama kasuwa mafi girma a duniya ga nau’in motoci. Idan an lura, za a ga karin motoci masu aiki da lantarki da ke wucewa a titunan sassa daban daban na kasar, baya ga kuma karin na’urorin da aka kafa domin yi wa motocin caji.

  • Ranar Muhalli Ta Farko Ta Kasar Sin Za Ta Amfani Duniya Baki Daya

Hakika, bunkasuwar motoci masu aiki da lantarki wani bangare ne kawai na ci gaban kasar Sin ta fannin kiyaye muhalli. A cikin shekaru 10 da suka wuce, kasa da kasa sun kuma shaida yadda kasar ta zama kasar ta fi yawan karuwar dazuzzuka a duniya, da kasar ta fi saurin inganta iskarta, baya ga yadda ta kasance kasar da ta fi yin tsimin makamashi da raya sabbin makamashi a duniya. Duk wadannan sun faru ne sakamakon yadda manufar nan ta “kyakkyawan muhalli shi ne kadarori masu kima” ke kara zame wa Sinawa jini da tsoka a rayuwarsu ta yau da kullum, manufar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a ranar 15 ga watan Agustan shekarar 2005, wanda a lokacin ya kasance sakataren kwamitin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin reshen lardin Zhejiang da ke gabashin kasar. Sakamakon manufar, a cikin shekaru 18 da suka wuce, duniya ta shaida yadda kasar Sin ta yi ta kara kyaunta, haka kuma ta samar da gudummawar kasar Sin ga kyautata muhallin halittu na duniya baki daya.

In mun dauki sabbin makamashi a misali, a cikin shekaru 10 da suka wuce, kasar Sin ta zamanto ta farko a duniya ta fannin samar da sabbin makamashi, don haka ma, ya zama muhimmin bangaren kasar Sin ke aiwatar da hadin gwiwa da kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka.

A yankin De Aar da ke tsakiyar kasar Afirka ta kudu, fararen na’urorin samar da wutar lantarki da makamashin iska, suna samar da lantarki sama da KW miliyan 750 a kowace shekara, kuma ta hakan an yi tsimin kwal kimanin tan sama da dubu 200, tare da rage fitar da iskar Carbon kimanin tan dubu 700. Sai kuma a yankin Garrisa na kasar Kenya, kamfanin kasar Sin ya kafa tashar samar da lantarki da makamashin rana irinta mafi girma a gabashin Afirka, wanda ya sassauta matsalar karancin wutar lantarki da kasar ta fuskanta, amma kuma ba tare da fitar da iskar Carbon ba. A kasar Nijeriya kuma, kamfanin kera bas bas na Yutong na kasar Sin, ya samar da bas bas masu aiki da wutar lantarki a birnin Lagos, karon farko ke nan da kasar ta shigo da bas bas masu aiki da sabbin makamashi.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A kokarin da kasar Sin ke yi, an kaddamar da jerin shirye-shirye na tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba a dimbin kasashe masu tasowa, wadanda suka sa kaimin kyautata muhallin halittun duniya.

Duniyarmu gida ne na bai daya ga dukkanin ‘yan Adam, kuma ‘yan Adam makomarsu daya ce a yayin da suke fuskantar matsalolin muhalli. A yayin da kasar Sin ke ci gaba da inganta muhallin halittu na cikin gida, za ta kuma ci gaba da samar da gudummawarta, ta hada hannu da sassan kasa da kasa, musamman ma kasashen Afirka, don kara inganta muhallin duniyarmu ta bai daya. (Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamman Zamfara Ya Rantsar Da Kwamishinoni 18 Tare Raba Musu Ma’aikatu

Next Post

Juyin Mulki: Hafsoshin Sojin ECOWAS Za Su Cimma Matsaya A Kan Nijar

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

16 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

17 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

19 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

22 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

23 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

1 day ago
Next Post
ECOWAS Ta Gargadi Sojin Nijar A Kan Hukunta Bazoum

Juyin Mulki: Hafsoshin Sojin ECOWAS Za Su Cimma Matsaya A Kan Nijar

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kasar Sin

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.