• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasashen Afirka Za Su Iya Rage Illar Harajin Amurka

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Kasashen Afirka Za Su Iya Rage Illar Harajin Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan kawo karshen yakin duniya na biyu, Amurka ta yi gwagwarmayar tabbatar da ‘yancin kasuwanci a duniya wajen kafa tsare-tsare da suka kunshi bangarori daban-daban ta hanyar Babbar Yarjejeniyar Haraji da Cinikayya ta GATT, har daga bisani aka samar da Hukumar Kasuwanci ta Duniya (WTO). To, sai dai kuma, matakan da ta dauka kwanan nan na kare-karen haraji da dabarun kariyar cinikayya sun zama abin kunya, tare da bata rawarta da tsalle.

 

Mummunan tasirin matakan nata ba kawai ya tsaya ga karin haraji ba ne kadai, nema take ko ta halin kaka sai ta mamaye batun ci gaban fasaha a duniya. Tun daga zuwan Trump a farkon shekarar nan, kasar ta ci gaba da aiwatar da tsauraran matakan kariyar fasaha, da dankwafar da kasashe masu tasowa da karin matsin lamba ga manyan kasashe.

  • Gwamnatin Kano Ta Fidda Sabbin Dokoki Domin Yaƙi Da Gurɓata Muhalli
  • Zuba Jari Daga Kasashen Waje A Noman Zamani: Jigawa Ta Baje Kolin Aikin Noma A Abuja

Kasar Sin ta sha daukar matakai don mayar da martani ga Amurka, haka nan sauran kasashe masu kumbar susa, amma kasashenmu na Afirka, musamman ma wadanda suka fi dogaro da kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasuwannin Amurka, me za su yi?

 

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Dokar bunkasa ci gaban Afirka da samar da dama ga yankin (AGOA), wacce ta bai wa kasashen yankin damar fitar da kayayyaki zuwa Amurka ba tare da haraji ba, ta shiga gararamba bisa yadda karin harajin zai kassara masana’antu kamar su masaku, da na karafa, da kuma noma.

 

Nijeriya da Afirka ta Kudu da suka fi karfin tattalin arziki a yankin, Amurka ta kakaba musu haraji na kaso 14% da 30% bi-da-bi, saboda rashin imani kuma karamar kasa kamar Lesotho wacce du-du-du karfin tattalin arzikinta na GDP bai wuce dala biliyan 2 ba, aka dankara mata karin harajin da kashi 50%.

 

Galibin tattalin arzikin kasashen Afirka ya fi dogaro ne da fitar da kayayyaki zuwa ketare don dorewar samar da aikin yi da kudaden shiga ga gwamnatoci, to amma kuma yanzu Amurka ta zama kadangaren bakin tulu. Babu makawa kasashen Afirka su kara karkata zuwa kasar Sin da sauran kasuwanni don samun damammakin cinikayya. Kamar yadda Shugaban Ghana John Mahama ya bayyana kwanan baya, wadannan sauye-sauye da ake samu kwanan nan na iya zama alheri ga Afirka ta hanyar dogaro da kansu.

 

Kasashen Afirka za su iya amfani da yanayin da ake ciki wajen zurfafa alaka da Sin, wadda ta kara habaka kasuwancinta da zuba jari a duk fadin nahiyar. A maimakon kari, ita kasar Sin ta bullo da manufar cire harajin ne ma ga kasashen Afirka 33 da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki, da ba da damar shiga kasuwanninta. Wannan ya bude sabbin damammakin ga masana’antun Afirka su fitar da kayayyakinsu zuwa kasar musamman a fannin noma.

 

Haka nan, kasashen Afirka za su iya yin hadin gwiwa da kasar Sin don inganta kasuwancinsu a bangaren fasahohin zamani wadda duniya ke kara karkata a kai, inda hakan zai karfafa samar da tsarin cinikayya ta intanet da bude sabbin kasuwanni masu amfani da fasaha.

 

Da yake yawancin kasashen Afirka sun riga sun karbi shawarar ziri daya da hanya daya na BRI, wanda ke samar da kudade don ayyukan more rayuwa, za su iya amfani da wannan ma don kara karfafa hada-hadar sufuri da kyautata huldar cinikayya da za su kara musu kwarin gogayya da sauran shiyyoyin duniya. Bugu da kari, gwamnatocin Afirka na iya karfafa ‘yan kasuwa na gida su shiga cikin hadin gwiwar da suke kullawa da Sin don karfafa masana’antu na cikin gida.

 

Tabbas, ta hanyar yin cudanya da kasar Sin bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni masu dacewa, kasashen Afirka za su iya rage illar kare-karen harajin Amurka, da samar da daidaiton huldar cinikayya mai tallafa wa ci gaban tattalin arzikinsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Fidda Sabbin Dokoki Domin Yaƙi Da Gurɓata Muhalli

Next Post

Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Zakarun Turai A Karon Farko Bayan Shekaru 10

Related

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

4 minutes ago
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

1 hour ago
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

2 hours ago
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

3 hours ago
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

4 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Daga Birnin Sin

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

6 hours ago
Next Post
Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Zakarun Turai A Karon Farko Bayan Shekaru 10

Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Zakarun Turai A Karon Farko Bayan Shekaru 10

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.