• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

by Muhammad
3 months ago
Kano

Ana zargin Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, da karɓar kuɗin toshiyar baki har Dala 30,000 daga wani ƙasurgumin dilan ƙwaya, Sulaiman Danwawu, domin yim belinsa a kotu, kamar yadda rahoton da Hukumar Tsaro ta Ƙasa (SSS), ta fitar.

An taɓa ayyana Namadi a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo saboda zargin aikata zamba a shekarar 2013, kafin daga bisani Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa shi a matsayin Kwamishina.

  • An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
  • Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Majiyoyin SSS daga Abuja sun shaida wa DAILY NIGERIAN cewa an gudanar da bincike a asirce kan batun, kuma hukumar ta shawarci gwamna da ya sauke Namadi daga muƙaminsa.

Yadda Ake Zargin Ya Karɓi Kuɗin

A cewar rahoton, Namadi ya karɓi Dala 30,000 kafin ya amince ya tsayawa Danwawu a kotu.

Wannan na nufin ya ɗauki alhakin cewa Danwawu ba zai tsere ba bayan bayar da shi beli.

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Bayan mutane da dama sun nuna ɓacin ransu kan al’amarin, gwamna Abba Yusuf ya kafa kwamiti domin bincikar lamarin, tare da umarnin a miƙa masa rahoton cikin mako guda.

Gwamnan, ya taɓa goyon bayan jami’an tsaro wajen kama Danwawu, kuma ya umarci NDLEA ka da su sake shi.

Wani jami’i ya ce: “Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ɗauki wannan aiki na Kwamishina a matsayin cin fuska ga gwamnatinsa da kuma yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi.”

An ruwaito cewar gwamnatin Jihar Kano ta shirya wani shiri a ɓoye domin kama Danwawu, wanda Kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Bakori ya jagoranta.

Me Ya Sa Gwamnan Bai Kore Shi Ba?

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi niyyar korar Namadi nan take, amma ya dakatar da hakan bayan ganawa da jagoran NNPP, Sanata  Rabiu Musa Kwankwaso, wanda shi ne ya bayar da sunan Namadi domin naɗa shi a matsayin Kwamishina.

Wasu majiyoyi sun ce gwamnan bai so naɗa Namadi ba tun da farko, amma saboda girmamawa da biyayya ga Kwankwaso ya ba shi muƙami.

Wani hadimina cikin gwamnatin ya ce: “Kwamishinan yana matsala da shugaban ƙungiyar direbobi ta NURTW, Kabiru Labour, saboda ƙoƙarin tilasta musu biyan harajin Naira 500,000 a kowane wata.”

“Haka kuma, Kwamishinan na gudanar da harkokin ma’aikatar ba tare da haɗin kai da sakatarenta Abdulmumin Babani ba. Saboda haka, sama da takardu 30 daga Ma’aikatar Sufuri ba su samu amincewar gwamna ba.”

Majiyar tace saboda rashin jituwa da kuma gazawar shugabancinsa, gwamnan yanke kauce wa hulɗa da ma’aikatar.

Martanin Namadi

Da aka tambayi Namadi, ya ce: “Ban san da wancan zargin ba, kuma ba gaskiya ba ne.”

Sai dai ba da jimawa ba, Kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Ibrahim Waiya, ya ce an kawo ƙarshen lamarin.

Cikin fushi ya bayyana cewa: “Wane irin aikin jarida kake yi ne haka? Me ya sa kake bin wannan batun babu ƙaƙƙautawa? Me kake nema ne?”

Yadda Lamarin Ya Samo Asali

A ranar 24 ga watan Yuli, DAILY NIGERIAN ta fyadda Namadi ne ya taimaka wajen belin Danwawu, bayan kotu ta sanya masa sharuɗa masu tsauri.

A ranar 16 ga watan Yuli, kotu ta amince da buƙatar beli, amma ta buƙaci sai an samu Kwamishina a cikin majalisar zartarwa ta Jihar Kano da zai tsaya masa, tare da biyan Naira 5,000,000.

Namadi ne ya tsaya masa, ta hanyar rubuta wasiƙa zuwa kotun a ranar 18 ga watan Yuli, 2025, yana neman a amince masa domin ya tsawa wanda ake zargi.

Wasiƙar da jaridar DAILY NIGERIAN ta samu ta nuna cewa ya ce: “Ina roƙon kotu mai daraja da ta yadda na tsaya wa wanda ake tuhuma da laifi, Sulaiman Aminu, wanda aka bayar da beli kan kuɗi Naira 3,000,000 da kuma wanda zai tsaya masa. Sannan ya ajiye Naira 5,000,000.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
Manyan Labarai

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
Next Post
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.