• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

by Muhammad
2 months ago
in Labarai
0
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana zargin Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, da karɓar kuɗin toshiyar baki har Dala 30,000 daga wani ƙasurgumin dilan ƙwaya, Sulaiman Danwawu, domin yim belinsa a kotu, kamar yadda rahoton da Hukumar Tsaro ta Ƙasa (SSS), ta fitar.

An taɓa ayyana Namadi a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo saboda zargin aikata zamba a shekarar 2013, kafin daga bisani Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa shi a matsayin Kwamishina.

  • An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
  • Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Majiyoyin SSS daga Abuja sun shaida wa DAILY NIGERIAN cewa an gudanar da bincike a asirce kan batun, kuma hukumar ta shawarci gwamna da ya sauke Namadi daga muƙaminsa.

Yadda Ake Zargin Ya Karɓi Kuɗin

A cewar rahoton, Namadi ya karɓi Dala 30,000 kafin ya amince ya tsayawa Danwawu a kotu.

Wannan na nufin ya ɗauki alhakin cewa Danwawu ba zai tsere ba bayan bayar da shi beli.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Bayan mutane da dama sun nuna ɓacin ransu kan al’amarin, gwamna Abba Yusuf ya kafa kwamiti domin bincikar lamarin, tare da umarnin a miƙa masa rahoton cikin mako guda.

Gwamnan, ya taɓa goyon bayan jami’an tsaro wajen kama Danwawu, kuma ya umarci NDLEA ka da su sake shi.

Wani jami’i ya ce: “Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ɗauki wannan aiki na Kwamishina a matsayin cin fuska ga gwamnatinsa da kuma yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi.”

An ruwaito cewar gwamnatin Jihar Kano ta shirya wani shiri a ɓoye domin kama Danwawu, wanda Kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Bakori ya jagoranta.

Me Ya Sa Gwamnan Bai Kore Shi Ba?

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi niyyar korar Namadi nan take, amma ya dakatar da hakan bayan ganawa da jagoran NNPP, Sanata  Rabiu Musa Kwankwaso, wanda shi ne ya bayar da sunan Namadi domin naɗa shi a matsayin Kwamishina.

Wasu majiyoyi sun ce gwamnan bai so naɗa Namadi ba tun da farko, amma saboda girmamawa da biyayya ga Kwankwaso ya ba shi muƙami.

Wani hadimina cikin gwamnatin ya ce: “Kwamishinan yana matsala da shugaban ƙungiyar direbobi ta NURTW, Kabiru Labour, saboda ƙoƙarin tilasta musu biyan harajin Naira 500,000 a kowane wata.”

“Haka kuma, Kwamishinan na gudanar da harkokin ma’aikatar ba tare da haɗin kai da sakatarenta Abdulmumin Babani ba. Saboda haka, sama da takardu 30 daga Ma’aikatar Sufuri ba su samu amincewar gwamna ba.”

Majiyar tace saboda rashin jituwa da kuma gazawar shugabancinsa, gwamnan yanke kauce wa hulɗa da ma’aikatar.

Martanin Namadi

Da aka tambayi Namadi, ya ce: “Ban san da wancan zargin ba, kuma ba gaskiya ba ne.”

Sai dai ba da jimawa ba, Kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Ibrahim Waiya, ya ce an kawo ƙarshen lamarin.

Cikin fushi ya bayyana cewa: “Wane irin aikin jarida kake yi ne haka? Me ya sa kake bin wannan batun babu ƙaƙƙautawa? Me kake nema ne?”

Yadda Lamarin Ya Samo Asali

A ranar 24 ga watan Yuli, DAILY NIGERIAN ta fyadda Namadi ne ya taimaka wajen belin Danwawu, bayan kotu ta sanya masa sharuɗa masu tsauri.

A ranar 16 ga watan Yuli, kotu ta amince da buƙatar beli, amma ta buƙaci sai an samu Kwamishina a cikin majalisar zartarwa ta Jihar Kano da zai tsaya masa, tare da biyan Naira 5,000,000.

Namadi ne ya tsaya masa, ta hanyar rubuta wasiƙa zuwa kotun a ranar 18 ga watan Yuli, 2025, yana neman a amince masa domin ya tsawa wanda ake zargi.

Wasiƙar da jaridar DAILY NIGERIAN ta samu ta nuna cewa ya ce: “Ina roƙon kotu mai daraja da ta yadda na tsaya wa wanda ake tuhuma da laifi, Sulaiman Aminu, wanda aka bayar da beli kan kuɗi Naira 3,000,000 da kuma wanda zai tsaya masa. Sannan ya ajiye Naira 5,000,000.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Kabir YusufDanwawuDilan ƘwayaGwamnakanoKwamishinaNamadiZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Next Post

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

5 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

18 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

21 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

24 hours ago
Next Post
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.