• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda LEADERSHIP Da Gwamnatin Nasarawa Suka Jagoranci Horas Da Matasa 100 San’o’in Dogaro Da Kai

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Leadership

Kamfani LEADERSHIP da hadin gwiwar Gwamnatin Jihar Nasarawa sun kaddamar da ba da horo ga matasa a fannin koyar da sana’o’i daba-daban a karkashin shirin Gwamnatin Shugaba Kasa Bola Ahmed Tinubu na tsamo ‘yan Nijeriya miliyan biyu daga kangen talauci.

Matasa 100 ne suka ci gajiyar shirin wadanda dukkaninsu mata ne da suka fito daga Jihar Nasarawa. An gudanar da wannan horo ne a Babban Birnin Tarayya Abuja, inda aka koyar sana’o’in da suka hada da; yadda ake noman kifin da kaji da yadda ake ciyar da su, kiwon zuma, koyar da ilimin fasahar sadarwa. Sauran sana’o’in sun hada koyar da sana’ar takalma, yadda ake yin kamfala, koyar da sana’ar takalma.

  • Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano
  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar

Da yake magana a yayin kaddamar da shirin, Babban Editan Rukunin Kamfanin LEADERSHIP Mr Azu, ya bayyana jin dadinsa tare da gamsuwarsa da wannan shiri, inda ya ce “Ko shakka babu yau LEADERSHIP muna cikin farin ciki domin kaiwa ga wannan matakin farkon cikin abin da muke buri.”

“Bugu da kari, muna matukar godiya ga Zababben Gwamnan Jihar Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi A Sule, sakamakon amincewa da ya yi da wannan muhimmin shiri da zai taimaka wajen tsamo ‘yan Nijeriya miliyan biyu daga kangin talauci, tare da zabo mutum 100 wadanda za su amfana da shirin bisa dacewa kuma cikin gaggawa, babu shakka wannan ya tabbatar da nuna sadaukar da kai cikin ayyukan da suka shafi al’umma,”in ji shi.

Ya ba da misali kan wasu adadi da Hukumar Kididdiga ta Kasa NBA ta fitar inda ta bayyana cewa, ‘yan Nijeriya yawan ‘yan Nijeriya marasa aikin yi ya kai kashi 5.3 cikin 100, kuma wannan kididdiga ba ta tsaya a miliyoyin ‘yan Nijeriya da ba su da aiki yi kadai ba, lamarin ya shafi iyalai da ke fadin kasar nan wadanda ba sa iya sayawa ‘ya’yansu barin biredi, ko mudun shinkafa ko madara.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

A karshe ya bayyana fatansa akan wannan shiri, inda ya ce wannan horarwa za ta iya hada abubuwan da aka koya muku domin amfanin kanku.

Wakilinmu ya samu zantawa da wasu daga wadanda suka ci gajiyar shirin inda suka bayyana masa irin godiya da farin ciki gami da addu’ar da suka yi Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da bullo da shirin. Sannan kuma suka nuna godiya ga Gwamnatin Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya A A Sule bisa jajircewarsa wajen ganin ya zama na farko wajen aiwatar da wanna shiri a fadin kasar nan.

Fatima Musa daga cikin wadanda suka gajiyar wannan shiri wadda ta zo a bangaren wadanda aka koyawa sana’ar Rini da Bugu, wato yadda za su sarrafa farin kaya ya koma launin Kamfala. Ta yi godiya ga Gwamantin A A Sule bisa wannan dama da ta bata, inda ta ce ba ta tsammanin za ta tsinci kanta a wannan shiri ba. “ A yanzu na samu sana’ar da zan dogara da kaina kuma ina fatan nan da wani lokaci in koyawa wasu suma su tsaya da kafarsu.

Haka ita ma Aisha Yakubu, na daga cikin wadanda suka gajiyar wannan shirin na koyon sana’o’i, wacce ta samu horo kan yadda za a sarrafa abincin kaji da kifi, da kuma yadda ake nomansu, cewa ta yi, babu abin da za su cewa gwamnatin mai girma A A Sule sai dai addu’ar Allah ya sa ya gama da duniya lafiya.

Ita kuwa Hajiya Amina Muhammad wadda ta samu shiga cikin shirin wacce ta mafana da horo a fannin koyon noman Zuma, ta ce, wannan shiri ta samu ilimi sosai ganin yadda Gwamnatin A A Sule ta yi tsayin daka wajen ganin ya taimaka wa matasa musamman mata domin su tsaya da kafarsu.

Sannan ta yi godiya ga Gwamnatin Shugaba Tinubu a matsayinsa na wanda ya yi tunanin yadda za a tsamo ‘yan Nijeriya daga kangin talauci.

Haka zalika Abubakar Ruth, matashiya ce da ta koyi yadda ake kera Jaka da Takalma, cewa ta yi, “A matsayinta na matashiya kuma talaka a yanzu babu abin da za ta maida hankali a kai illa ganin ya habaka wannan sana’a, inda a karshe ta yi godiya ga shugaban Kasa da kuma Gwamnan Jihar Nasarawa AA Sule bisa hangen nesansu na kokarin karfafa wa matsa musamman ma mata a wannan yanayi da ake ciki na kuncin rayuwa.”

Daga cikin wadanda suka albarkaci taron budewa da rufewa, sun hada da Babban Edita, kuma Babban Mataimaki ga Shugabar Kamfanin LEADERSHIP Mista Azubuke, da Mataimakin shugaban kamfanin Mike Okpere, sai kuma Babban Manajan Darakta Na Rukunin Kamfanin LEADERSHIP Malam Mu’azu Elazeh, da Darakta a LEADERSHIP Abraham Nda Isiah. Bayan kammala ba da wannan horo ne kamfanin LEADERSHIP na ya ba da takardar shaida ga dukkan daliban da suka samu halartar wannan horo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Next Post
Matakan Sin Na Daga Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

Matakan Sin Na Daga Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.