• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda LEADERSHIP Da Gwamnatin Nasarawa Suka Jagoranci Horas Da Matasa 100 San’o’in Dogaro Da Kai

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Labarai
0
Yadda LEADERSHIP Da Gwamnatin Nasarawa Suka Jagoranci Horas Da Matasa 100 San’o’in Dogaro Da Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfani LEADERSHIP da hadin gwiwar Gwamnatin Jihar Nasarawa sun kaddamar da ba da horo ga matasa a fannin koyar da sana’o’i daba-daban a karkashin shirin Gwamnatin Shugaba Kasa Bola Ahmed Tinubu na tsamo ‘yan Nijeriya miliyan biyu daga kangen talauci.

Matasa 100 ne suka ci gajiyar shirin wadanda dukkaninsu mata ne da suka fito daga Jihar Nasarawa. An gudanar da wannan horo ne a Babban Birnin Tarayya Abuja, inda aka koyar sana’o’in da suka hada da; yadda ake noman kifin da kaji da yadda ake ciyar da su, kiwon zuma, koyar da ilimin fasahar sadarwa. Sauran sana’o’in sun hada koyar da sana’ar takalma, yadda ake yin kamfala, koyar da sana’ar takalma.

  • Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano
  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar

Da yake magana a yayin kaddamar da shirin, Babban Editan Rukunin Kamfanin LEADERSHIP Mr Azu, ya bayyana jin dadinsa tare da gamsuwarsa da wannan shiri, inda ya ce “Ko shakka babu yau LEADERSHIP muna cikin farin ciki domin kaiwa ga wannan matakin farkon cikin abin da muke buri.”

“Bugu da kari, muna matukar godiya ga Zababben Gwamnan Jihar Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi A Sule, sakamakon amincewa da ya yi da wannan muhimmin shiri da zai taimaka wajen tsamo ‘yan Nijeriya miliyan biyu daga kangin talauci, tare da zabo mutum 100 wadanda za su amfana da shirin bisa dacewa kuma cikin gaggawa, babu shakka wannan ya tabbatar da nuna sadaukar da kai cikin ayyukan da suka shafi al’umma,”in ji shi.

Ya ba da misali kan wasu adadi da Hukumar Kididdiga ta Kasa NBA ta fitar inda ta bayyana cewa, ‘yan Nijeriya yawan ‘yan Nijeriya marasa aikin yi ya kai kashi 5.3 cikin 100, kuma wannan kididdiga ba ta tsaya a miliyoyin ‘yan Nijeriya da ba su da aiki yi kadai ba, lamarin ya shafi iyalai da ke fadin kasar nan wadanda ba sa iya sayawa ‘ya’yansu barin biredi, ko mudun shinkafa ko madara.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

A karshe ya bayyana fatansa akan wannan shiri, inda ya ce wannan horarwa za ta iya hada abubuwan da aka koya muku domin amfanin kanku.

Wakilinmu ya samu zantawa da wasu daga wadanda suka ci gajiyar shirin inda suka bayyana masa irin godiya da farin ciki gami da addu’ar da suka yi Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da bullo da shirin. Sannan kuma suka nuna godiya ga Gwamnatin Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya A A Sule bisa jajircewarsa wajen ganin ya zama na farko wajen aiwatar da wanna shiri a fadin kasar nan.

Fatima Musa daga cikin wadanda suka gajiyar wannan shiri wadda ta zo a bangaren wadanda aka koyawa sana’ar Rini da Bugu, wato yadda za su sarrafa farin kaya ya koma launin Kamfala. Ta yi godiya ga Gwamantin A A Sule bisa wannan dama da ta bata, inda ta ce ba ta tsammanin za ta tsinci kanta a wannan shiri ba. “ A yanzu na samu sana’ar da zan dogara da kaina kuma ina fatan nan da wani lokaci in koyawa wasu suma su tsaya da kafarsu.

Haka ita ma Aisha Yakubu, na daga cikin wadanda suka gajiyar wannan shirin na koyon sana’o’i, wacce ta samu horo kan yadda za a sarrafa abincin kaji da kifi, da kuma yadda ake nomansu, cewa ta yi, babu abin da za su cewa gwamnatin mai girma A A Sule sai dai addu’ar Allah ya sa ya gama da duniya lafiya.

Ita kuwa Hajiya Amina Muhammad wadda ta samu shiga cikin shirin wacce ta mafana da horo a fannin koyon noman Zuma, ta ce, wannan shiri ta samu ilimi sosai ganin yadda Gwamnatin A A Sule ta yi tsayin daka wajen ganin ya taimaka wa matasa musamman mata domin su tsaya da kafarsu.

Sannan ta yi godiya ga Gwamnatin Shugaba Tinubu a matsayinsa na wanda ya yi tunanin yadda za a tsamo ‘yan Nijeriya daga kangin talauci.

Haka zalika Abubakar Ruth, matashiya ce da ta koyi yadda ake kera Jaka da Takalma, cewa ta yi, “A matsayinta na matashiya kuma talaka a yanzu babu abin da za ta maida hankali a kai illa ganin ya habaka wannan sana’a, inda a karshe ta yi godiya ga shugaban Kasa da kuma Gwamnan Jihar Nasarawa AA Sule bisa hangen nesansu na kokarin karfafa wa matsa musamman ma mata a wannan yanayi da ake ciki na kuncin rayuwa.”

Daga cikin wadanda suka albarkaci taron budewa da rufewa, sun hada da Babban Edita, kuma Babban Mataimaki ga Shugabar Kamfanin LEADERSHIP Mista Azubuke, da Mataimakin shugaban kamfanin Mike Okpere, sai kuma Babban Manajan Darakta Na Rukunin Kamfanin LEADERSHIP Malam Mu’azu Elazeh, da Darakta a LEADERSHIP Abraham Nda Isiah. Bayan kammala ba da wannan horo ne kamfanin LEADERSHIP na ya ba da takardar shaida ga dukkan daliban da suka samu halartar wannan horo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HoroLEADERSHIPMatasaNasarawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Na Ji Bayan Faduwa Zaben 2015 – Jonathan 

Next Post

Matakan Sin Na Daga Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

Related

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

10 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

11 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

12 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

15 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

16 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

17 hours ago
Next Post
Matakan Sin Na Daga Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

Matakan Sin Na Daga Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.