• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Masana Ke Ankarar Da Kasashe Masu Tasowa Don Koyon Dabarun Yaki Da Fatara Daga Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Masana Ke Ankarar Da Kasashe Masu Tasowa Don Koyon Dabarun Yaki Da Fatara Daga Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa lura da irin manyan nasarorin da kasar Sin ta cimma a fannin yaki da fatara da kyautata yanayin zaman rayuwar alummun Sinawa, wannan batu yayi matukar jan hankalin duniya duba da girman alkaluman miliyoyin mutanen da kasar Sin ta tsame daga kangin talauci.

Hakika, masana na ganin cewa kasar Sin tana dora muhimmanci kan batun ayyukan kawar da talauci a cikin yankunan karkara, kuma ta cimma muradun neman ci gaba mai dorewa na MDD ta hanyar amfani da aikin gona na zamani, wannan a cewarsu, wata fasaha ce mai kyau da za ta taimakawa sauran kasashe masu tasowa da ma duniya baki daya.

  • Wakilan Yankin Hong Kong Na Kasar Sin Sun Bayyana Halin Da Ake Ciki A Yankin A Wajen Taron UNHRC

Idan zamu iya tunawa, a kwanakin baya ne aka shirya wani taro a birnin Qujing dake lardin Yunnan na kudu maso yammacin kasar Sin, domin bitar irin nasarorin da kasar Sin ta cimma a fannin kawar da talauci da raya yankunan karkara.

A yayin taron, an jiyo mataimakin firaministan kasar Sin, Hu Chunhua, ya yi kira da a kara kokarin karfafa nasarorin da aka cimma na yaki da talauci da tabbatar da aiwatar da manufofin da aka tsara na farfado da yankunan karkara domin samun moriya mai dorewa.

Wannan batu dai zamu iya cewa, zai jima a zukatan masu fashin baki da sharhi kan al’amurran zamantakewar rayuwar bil adama na kasa da kasa. Batun dai ya sa masanan kasa da kasa ke cigaba da bayyana ra’ayoyinsu game da wannan babban tagomashi da Sin ta samu.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

A kwanan nan, wani kwararren masani a Najeriya yace, nasarorin da kasar Sin ta cimma a yaki da fatara ta samar da wani muhimmin darasi da ya kamata kasashe maso tasowa su koya domin tsame dunbun al’ummunsu daga cikin yanayin kangin talauci a cikin kayyedadden lokaci.

A wata hirar da ya yi kwanan nan da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Abuja, babban birnin Najeriya, dakta Sheriff Ghali Ibrahim, shugaban sashen nazarin kimiyyar siyasa da huldar kasa da kasa na jami’ar Abuja, ya ce kasar Sin, a kokarinta na tsame sama da mutane miliyan 800 daga kangin fatara a cikin wasu ‘yan shekaru, ta yi amfani da dabaru na zahiri, kuma ta gwadawa duniya cewa ita jagora ce. Don haka, ya kamata kasashe masu tasowa musamman kasashen Afrika, da na Latin Amurka, da na Caribbean, su yi koyi da kasar Sin a shirinta na yaki da fatara.

A tsokacin da masanin ya yi ya ce, hangen nesan da kasar Sin ta yi, ya taka muhimmiyar rawa a shirinta na yaki da talauci, inda ya bukaci kasashe masu tasowa dake da dunbun albarkatun kasa, da su yi amfani da su wajen tsara dabarun yadda za su tinkari yaki da fatara a kasashensu.

Ko shakka babu, kasar Sin tana iyakar kokarinta wajen sauke nauyin alummarta, a hannu guda kuma, tana bada gagarumar gudunmawa ga cigaban kasa da kasa. Masana da dama sun bayyana kasar Sin a matsayin kasar da ta fi bada gudunmawa ga ci gaba mai dorewa a Afrika haka kuma babbar mai taimakawa kasashe masu tasowa.

Babban abinda ake fata dai shine, kasashen masu tasowa su yi koyi salo da kuma irin dabarun da Sin ke amfani dasu wajen tsamewa alummarta kitse daga wuta, dama masu hikimar magana na cewa, “daga na gaba ake gane zurfin ruwa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Allah Ya Yi Wa Wazirin Dogaran Zazzau Rasuwa

Next Post

An Gudanar Da Dandalin Cibiyoyin Ilimi Na Sin Da Afirka Na Shekarar 2022

Related

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

7 hours ago
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
Daga Birnin Sin

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

8 hours ago
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

9 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

10 hours ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

11 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

12 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Dandalin Cibiyoyin Ilimi Na Sin Da Afirka Na Shekarar 2022

An Gudanar Da Dandalin Cibiyoyin Ilimi Na Sin Da Afirka Na Shekarar 2022

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.