• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Masana Ke Ankarar Da Kasashe Masu Tasowa Don Koyon Dabarun Yaki Da Fatara Daga Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Masana Ke Ankarar Da Kasashe Masu Tasowa Don Koyon Dabarun Yaki Da Fatara Daga Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa lura da irin manyan nasarorin da kasar Sin ta cimma a fannin yaki da fatara da kyautata yanayin zaman rayuwar alummun Sinawa, wannan batu yayi matukar jan hankalin duniya duba da girman alkaluman miliyoyin mutanen da kasar Sin ta tsame daga kangin talauci.

Hakika, masana na ganin cewa kasar Sin tana dora muhimmanci kan batun ayyukan kawar da talauci a cikin yankunan karkara, kuma ta cimma muradun neman ci gaba mai dorewa na MDD ta hanyar amfani da aikin gona na zamani, wannan a cewarsu, wata fasaha ce mai kyau da za ta taimakawa sauran kasashe masu tasowa da ma duniya baki daya.

  • Wakilan Yankin Hong Kong Na Kasar Sin Sun Bayyana Halin Da Ake Ciki A Yankin A Wajen Taron UNHRC

Idan zamu iya tunawa, a kwanakin baya ne aka shirya wani taro a birnin Qujing dake lardin Yunnan na kudu maso yammacin kasar Sin, domin bitar irin nasarorin da kasar Sin ta cimma a fannin kawar da talauci da raya yankunan karkara.

A yayin taron, an jiyo mataimakin firaministan kasar Sin, Hu Chunhua, ya yi kira da a kara kokarin karfafa nasarorin da aka cimma na yaki da talauci da tabbatar da aiwatar da manufofin da aka tsara na farfado da yankunan karkara domin samun moriya mai dorewa.

Wannan batu dai zamu iya cewa, zai jima a zukatan masu fashin baki da sharhi kan al’amurran zamantakewar rayuwar bil adama na kasa da kasa. Batun dai ya sa masanan kasa da kasa ke cigaba da bayyana ra’ayoyinsu game da wannan babban tagomashi da Sin ta samu.

Labarai Masu Nasaba

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

A kwanan nan, wani kwararren masani a Najeriya yace, nasarorin da kasar Sin ta cimma a yaki da fatara ta samar da wani muhimmin darasi da ya kamata kasashe maso tasowa su koya domin tsame dunbun al’ummunsu daga cikin yanayin kangin talauci a cikin kayyedadden lokaci.

A wata hirar da ya yi kwanan nan da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Abuja, babban birnin Najeriya, dakta Sheriff Ghali Ibrahim, shugaban sashen nazarin kimiyyar siyasa da huldar kasa da kasa na jami’ar Abuja, ya ce kasar Sin, a kokarinta na tsame sama da mutane miliyan 800 daga kangin fatara a cikin wasu ‘yan shekaru, ta yi amfani da dabaru na zahiri, kuma ta gwadawa duniya cewa ita jagora ce. Don haka, ya kamata kasashe masu tasowa musamman kasashen Afrika, da na Latin Amurka, da na Caribbean, su yi koyi da kasar Sin a shirinta na yaki da fatara.

A tsokacin da masanin ya yi ya ce, hangen nesan da kasar Sin ta yi, ya taka muhimmiyar rawa a shirinta na yaki da talauci, inda ya bukaci kasashe masu tasowa dake da dunbun albarkatun kasa, da su yi amfani da su wajen tsara dabarun yadda za su tinkari yaki da fatara a kasashensu.

Ko shakka babu, kasar Sin tana iyakar kokarinta wajen sauke nauyin alummarta, a hannu guda kuma, tana bada gagarumar gudunmawa ga cigaban kasa da kasa. Masana da dama sun bayyana kasar Sin a matsayin kasar da ta fi bada gudunmawa ga ci gaba mai dorewa a Afrika haka kuma babbar mai taimakawa kasashe masu tasowa.

Babban abinda ake fata dai shine, kasashen masu tasowa su yi koyi salo da kuma irin dabarun da Sin ke amfani dasu wajen tsamewa alummarta kitse daga wuta, dama masu hikimar magana na cewa, “daga na gaba ake gane zurfin ruwa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Allah Ya Yi Wa Wazirin Dogaran Zazzau Rasuwa

Next Post

An Gudanar Da Dandalin Cibiyoyin Ilimi Na Sin Da Afirka Na Shekarar 2022

Related

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60
Daga Birnin Sin

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

48 minutes ago
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

21 hours ago
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
Daga Birnin Sin

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

22 hours ago
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
Daga Birnin Sin

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

23 hours ago
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

24 hours ago
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

2 days ago
Next Post
An Gudanar Da Dandalin Cibiyoyin Ilimi Na Sin Da Afirka Na Shekarar 2022

An Gudanar Da Dandalin Cibiyoyin Ilimi Na Sin Da Afirka Na Shekarar 2022

LABARAI MASU NASABA

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

August 5, 2025
Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

August 5, 2025
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.