ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Matashi Ya Yi Yunƙurin Hallaka Matarsa Don Ya Samu Damar Sace Mata Talabijin

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Matashi

Wani abun takaici ya nuna yadda wani matashi ɗan shekara 35 a duniya a jihar Bauchi, Tijjani Ahmadu Diye, ya kama matarsa da dukan tsiya har ma ya yi yunƙurin kasheta da tabarya kawai domin ya samu damar sace mata ‘talabijin’.

Yadda lamarin ya faru kuwa, a ranar 2 ga watan Disamba, ya fito cikin gidansu ya yi ta yekuwar cewa ‘yan fashi da makami sun shigo cikin gidan domin juya tunanin matarsa.

  • Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna
  • Da Ɗumi-Ɗumi: Jam’iyyar APC Ta Kori Shugabanta Na Jihar Bauchi, Aliyu Misau

Ana hakan ya shiga cikin ɗaki ya umarci matarsa da ta lulluɓe fuskatar da ƙyalle, inda ya fita waje ya sake dawowa cikin ɗakin shi ma fuskarsa a rufe, nan take ya rufe matar tasa da dukan tsiya da ciki har da mari domin ya samu nasarar yin awun gaba da talabijin ɗinsu da zimmar sayarwa domin ƙara jari a shagonsa.

ADVERTISEMENT

A wata sanarwa daga shalkwatar ‘yansandan jihar Bauchi ɗauke da sanya hannun CP Ahmad Muhammad Wakil ta yi ƙarin haske da cewa: “Cikin gaggawa bayan samun rahoton faruwar lamarin, jami’anmu sun dira wajen da abun ya faru inda suka ɗauki wacce aka jikkata zuwa asibitin kwararru da ke Bauchi inda a halin yanzu take amsar kulawar likitoci.”

“Bincike farko-farko ya nuna yadda wanda ake zargin ya amsa laifinsa ba tare da wani ɓata lokaci ba. A amsa laifin nasa, wanda ake zargin ya yi yekuwar ƙarya na cewa ‘yan fashi da makami sun shiga cikin gidansu.”

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

“Wanda ake zargin ya kuma bayyana cewar niyyarsa shi ne ya kashe matarsa domin ya samu damar ɗaukan talabijin dinsu domin ya sayar ya samu kuɗin ƙara jari a shagonsa,” sanarwar ta ce.

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Auwal Musa Muhammad ya umarci a mayar da kes ɗin zuwa sashin binciken manya laifuka domin fadada bincike da gano haƙiƙanin abun da ya faru na cewa abun da mutumin ya faɗa haka ne ko akasinsa.

Sanarwar ta ce, bayan an kammala gudanar da bincike, za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kuliya manta sabo domin fuskantar doka daidai da laifin da ya aikata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Biya Wadanda Ta Yi Wa Rusau Diyyar N3bn

Gwamnatin Kano Za Ta Biya Wadanda Ta Yi Wa Rusau Diyyar N3bn

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.