ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Kula Da Gyambo Ke Cinye Kashi

by Sani Anwar
10 months ago
Concept with Health care And Medicine. black and white

Concept with Health care And Medicine. black and white

Idan aka yi buris, ta hanyar kin kula da rauni, miki ko gyambo a wani sashe na jiki; ba tare da bin hanyar magance shi ba, hakan zai iya jawo shigar kwayoyin cutar bakteriya ko fungai cikin wannan rauni.

Da zarar wadannan kwayoyin cututtuka sun shiga rauni, daga nan ne kuma sai raunin ya zama gyambo. Sannan, kamar yadda aka sani ne; alamomin gyambo sun hada da kumburi, ciwo, dumi, sauyin launin fata, lalacewar tsoka, taruwar mugunyar ruwa ko jinni ko kuma diwa.

  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Gwaji A Kan Fasahar Sadarwa
  • ‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya

Har ila yau, idan gyambo na kusa da gaba; yana iya jawo rikewar gaba da kuma wahalar motsa ta, sai dai da kyar ko da ‘yan dabaru.

ADVERTISEMENT

Idan kuwa har aka yi buris da gyambon, kwayoyin cututtuka babu wuya za su kutsa cikin wannan gyambo; har su kai ga kama kashi da bargon kashin baki-daya cikin kankanin lokaci.

Haka zalika, a yayin da kwayoyin cututtuka suka kama kashi da bargo, lamari ne da babu wani bata lokaci da ke bukatar kulawa ta musamman, domin kuwa a wannan lokaci lamarin ya canza kai tsaye zuwa cutar kashi, (Osteomyelitis) a turance.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Don haka, ‘Osteomyelitis’; cutar kashi ce wadda idan ba a yi kokarin shawo kanta da wuri ba, na barazanar rage ingancin kashi ko lalata shi ma baki-daya. Kazalika, idan cutar ta tsananta; tana iya cinye kashin wannan sashen gaba kwata-kwata.

Bugu da kari, bayan cutar kashi da gyambo; haka nan wadanda aka yi wa tiyatar kashi su ma suna iya gamuwa ko samun wannan cuta ta kashi, idan aka samu akasi wajen shigar wadannan kwayoyin cututtuka; yayin ko bayan aiwatar da tiyata.

Saboda haka, da zarar mutum ya yi rauni ko ya samu miki; akwai bukatar gaggawar tuntubar likita, domin samun kulawarsa don guje wa afkawar wadannan kwayoyin cututtuka da kuma kiyaye wannan cuta ta kashi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha
Kiwon Lafiya

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
Kiwon Lafiya

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

October 11, 2025
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Gudanar Da Liyafar Sabuwar Shekara

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Gudanar Da Liyafar Sabuwar Shekara

LABARAI MASU NASABA

APC

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.