• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Tsaftar Cikin Gida Ke Haifar Da kananan Cututtuka

by Bilkisu Tijjani
7 months ago
in Madubin Rayuwa
0
Yadda Rashin Tsaftar Cikin Gida Ke Haifar Da kananan Cututtuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin Taskira shafi ne da ya saba zakolo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma na yau da kullum. Tsokacimmu na yau zai yi duba ne game da rashin tsaftar cikin gida wadanne irin cututtuka ke haifarwa?

Usman Sani

Rashin tsaftar cikin gida yana haifar da kananan cututtuka ta hanyar jawo yaduwar kwayoyin cuta, kamar su kwayoyin da ke haddasa ciwon ciki, zazzavi, da gudawa. Guraren da ba a tsaftace ba suna jan hankalin kwari da dabbobi masu dauke da kwayoyin cuta.

  •  Ali Nuhu Ya Zama Jakadan Kamfanin Tsaftace HaÆ™ora A Arewacin Nijeriya 
  • Gudummawar Sin Ga Aikin Samar Da Duniya Mai Tsafta Da Kyan Gani

Wadanne hanyoyi za a bi don magance su?

Za a iya magance cututtukan da rashin tsafta ke haifarwa ta hanyar tsaftace muhalli akai-akai, amfani da ruwan sha mai tsabta, da tsaftace hannaye kafin cin abinci da bayan amfani da bayan gida. Haka nan, sanya shara a wuraren da suka dace da kuma tsaftace jikin dabbobin gida na taimakawa.

Labarai Masu Nasaba

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

Sajida Ahmad Ibrahim

Assalamu alaikum. Cututtukan da rashin tsaftar cikin gida take haifarwa.

Maleriya, kwalara, Tayipot, Amai, Godawa, cutar ciwon san yi da dai sauransu.

Ya kamata mu dage da tsaftace mahallimmu domin rashin tsafta gaskiya ba karamar illa bace kai zama a iya kiran rashin tsafta ba karamar masifa bace, ban da cututtuka da yake haifarwa, rashin tsafta ta kan sa mutane su rika kyamarka, rashin tsafta har aure yake kashewa.

Hanyoyin magance wannan cututtuka:

  1. wanke hannu bayan an fito daga bayan gida, wanke hannu kafin a ci abinci, sannan a yi Bisimillah.  
  2. Tsabtace ruwa kafin a yi amfani da shi a sha ko a yi girki. 
  3. Wanke bandaki akai-aka domin gujewa cututtuka. 
  4. Rufe abinci da tsabtace shi. 
  5. Kwana da gidan sauro ko wajen da ke da sauro. 
  6. Gyara kwatoci domin gujewa taruwar sauro
  7. Shara da wanke wanke domin gujewa taruwa kananan cuta da ba’a ganinsu.
  8. Rufe abinci da abin sha domin kada kudaje masu yada cutar kwalara su shiga ciki.

Hajiya Rukayya

Assalamu Alaikum Warahmatullah.                  

Gaskiya rashin tsaftar cikin gida na haifar da kanana da manyan cututtuka, Dalili kuwa shi ne, za ka ga mace ta fita gida tsaf amma cikin gidanta da kazanta, ga wanke-wanke ta barshi kuda na ta bi ga wanki ta jika yana ta wari, ga tsakar gidanta duk shara wanda hakan yana haifar da cututtuka irinsu Kwalara da Maleriya da dai sauransu don Allah mata mu gyara.

Daga Bilkisu Isma’il

Assalamu alaikum!

A gaskiya rashin tsafta cikin gida ba karamar cuta bace, saboda yana haifar da cututtuka da dama. Misali kamar Maleriya, Tayipot, Kwalara wato amai da gudawa cutar ciwon san yi na mata wanda wannan gaskiya ba karamar cuta bace, saboda idan cutar ta yi yawa har yana kai ga ya tava mahaifar mace, ki ga an zo ana ta wahala, wata ki ga ya zo ya kai ga har ana cewa ba za ta iya samun ciki ba saboda cutar ciwon san yi ya ci karfinta ya kashe mata mahaifa.

Wani sai ki ga an je asibiti ana cewa sai an yi mata wankin mahaifa, sai ki ga wata idan Allah ya sa an dace shikenan ta samu lafiya, wata kuma a yi ta yi har a gaji a barta. To kin ga gaskiya duka wadannan cututtuka da na lissafo ba kananu bane.

Ya kamata mata mu rage san jiki mutashi mu gyara gidajan kullum kar mu bar gidajanmu da kazanta. Ita kazanta tana kawo tsana tsakaninki da maigida koda kuwa shi bashi da tsafta, duk namiji ba ya san kazamar mace sai yaji duk tafita a ransa, mata mu gyara.

Hanyoyin da za ki gyara ki zama mai tsafta: Za ki iya kasa aikin gidanki, tsari ne abin, duk abin da kika yi amfani da shi kar ki bari wai sai kin zo shara a’a ki gyara wajen da take sai ki ga gidanki ba zai vaci ba. Kuma kullum ki kasance kina yi shara, ki koya wa ‘ya’yanki.

Sannan kar ki zama mai tara wanke-wanke, saboda shima babbar kazanta ce wani abu zai iya zuwa ya yi ta lasa miki kwano baki sani ba.

Faddausi Dahiru

Assalamu alaikum!

Rashin tsafta cikin gida gaskiya yana haifar da cututtuka da dama kuma banya cututtuka wadanda za su iya kashe mutum ma idan ba a yi taka tsantsan ba, kamar su Kwalara: Kwalara tana iya kashe mutum idan ya zo da karar kwana ki ga mutum yana ta amai da gudawa, mutum ya kare ya lalace cikin kwana guda idan Allah ma ya sa zai samu lafiya kenan, amma ana wahala idan ta kama mutum.

Maleriya: itama idan ta kama mutum, har ma idan ta ci karfin mutum ta wuce 1+, ana wahala za ki ga bata jin magani har sai an hada da allura.

Sai Tayipot shima idan ya kama mutum yana wahalar da shi. Abin da ke kawo shi rashin tsaftar ruwa, ko ka sha ruwa marar kyau ko kuma abin da a ka zuba ruwan bashi da kyau dayan biyu ne. Suna da yawa cututtukan, mata ya kamata mu daure, mu dage mu kuma jajirce wajen tsaftace muhallimmu, ke kanki idan kin tsaftar gidanki za ki ga kina yi jin dadin zama a ciki, sannan kuma iskar ma da za ta shigo za ki ji ta ta dabance mai dadi, babu wani wari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tsafta
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Gudanar Da Rahaza Karo Na 2 Na Shagalin Murnar Sabuwar Shekarar 2025 Bisa Kalandar Gargajiyar Kasar Sin

Next Post

Gwamna Radda Ya Yi Sauye-sauye A Majalisar Zartarwar Jihar Katsina

Related

Goron Sallah
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

3 weeks ago
GORON JUMA’A
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

4 weeks ago
Goron Sallah
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

2 months ago
GORON JUMA’A
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

3 months ago
GORON JUMA’A
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

4 months ago
Goron Sallah
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

5 months ago
Next Post
Gwamna Radda Ya Yi Sauye-sauye A Majalisar Zartarwar Jihar Katsina

Gwamna Radda Ya Yi Sauye-sauye A Majalisar Zartarwar Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

July 31, 2025
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

July 31, 2025
Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.