• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sulhun Shugabannin Al’umma Da ‘Yan Bindiga Ke Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

by Sani Anwar and Sulaiman
7 months ago
Kawayen amarya

Shugabannin al’umma a Kananan Hukumomin Jibiya, Batsari da Safana na Jihar Katsina, sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan bindigar da ke addabar kauyukansu.

Mazauna yankin sun ce, an yi zaman sulhun a baya-bayan nan tsakanin Shugabannin Karamar Hukumar Jibiya da ‘yan ta’adda a ranar Juma’a 28 ga watan Fabrairu, biyo bayan irin wannan yarjejeniyoyin da aka yi a Kananan Hukumomin Batsari da Safana, wadanda suka sha fama da hare-hare babu kakkautawa saboda kusancinsu da Dajin Rugga.

  • Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 
  • NPA Za Ta Yunkuro Don Zamanantar Da Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya – Dantsoho

Har ila yau, kamar yadda suka bayyana; tattaunawar ta samu halartar wakilan sojoji, jami’an tsaron farin kaya (DSS), ‘yansanda, jami’an sa ido na al’umma, ‘yan banga, sarakunan gargajiya da jami’an kananan hukumomi.

Kazalika, an bayyana cewa; wani sanannen shugaban ‘yan bindiga a yankin, Audu Lankai ne ya kaddamar da yarjejeniyar, inda ya nuna takaicinsa kan yadda rikicin ya dade ana yin sa.

Wata majiya mai tushe a Jibiya ta ce, “Babu hannun gwamanatin jihar kai tsaye a sulhun, domin kuwa gwamnan ya sha nanata cewa; ba zai tattauna da ‘yan bindiga ba, matukar ba su mika wuya sakamakon matsin lamba ba.”

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

“Amma a wannan karon, shugabannin al’ummarmu; sun gana da daya daga cikin manyan jami’an gwamnati, sannan sun ba mu goyon bayansu, bisa la’akari da halin da muke ciki.

Shugaban ‘yan bindigar Audu Lankai ne ya bukaci zaman wannan sulhu tare da bayyana cewa; ya gaji da wadannan tashe-tashen hankula da suke faruwa.

“Ya tuntubi daya daga cikin shugabanninmu, bayan tattaunawa mai tsawo, mun kuma amince da haduwa ranar Juma’a. Kazalika, mun amince da ci gaba da tattaunar zaman lafiya bayan Sallah, idan dukkanin bangarorin biyu suka mutunta sharuddan yarjejeniyar.”
Sharuddan da al’ummar Jibiya suka gindaya, sun hada da dakatar da hare-haren da ake kai wa matafiya a kan titin Jibiya zuwa Katsina, Batsari zuwa Batsari da kuma Jibia zuwa Gurbi da kuma kawo karshen hare-haren da ake kai wa kauyuka da garkuwa da mutane, barin manoma da mazauna yankunansu ci gaba da ayyukansu da sakin wadanda aka kama da kuma ajiye makamai.

Ya kara da cewa, ya zuwa yanzu an kubutar da mutum 11 da aka yi garkuwa da su, sannan ‘yan bindigar sun mika makamai biyu.

Majiyar ta kuma ce, ‘yan bindigar sun bukaci a bai wa ‘yan ta’addar damar shiga cikin al’umma, ba tare da wata barazana ga rayuwarsu ba, saboda bukatar kare kai daga kungiyoyin da ke gaba da juna da kuma wadanda ba ‘yan ta’adda ba.

A cikin wani faifan bidiyo, wani dan bindiga mai suna Bala Wuta, ya yi jawabi a makarantar firamare ta Kwari, inda ya koka da irin asarar da aka samu daga bangarorin biyu.

Ya bukaci gwamnati ta samar da ababen more rayuwa da suka hada da makarantu, wuraren ruwan sha da magunguna ga makiyaya, domin samun fahimtar juna.

Wani daga cikin shugabannin al’umma a Jibiya da bukaci a sake sunansa, ya tabbatar da yarjejeniyar zaman lafiyar, inda ya ce; “Hatta Annabi Muhammad SAW, ya shiga yarjejeniyar zaman lafiya, ma’ana wannan wani abu ne da Allah ya yarda da shi, domin kuwa; babu wata fa’ida a cikin rikici, idan bangarorin biyu na son kawo karshensa.

 

Zaman Lafiya Ya Fi Komai Dadi- Mazauna Kauyukan

Mazauna kauyukan da al’amarin ya shafa, sun bayyana jin dadinsu, inda suka bayyana cewa; shirin samar da zaman lafiyar da al’umma ke yi ya fara nuna kyakkyawan sakamako.

Haka zalika, sun bayyana cewa; yankunan da ake gani sun fi hatsarin ziyarta, sannu a hankali ana samun dawowar zaman lafiya na rayuwar yau da kullum.

Malam Yahuza Aliyu, Mataimakin Hakimin Kauyen Wagini a Karamar Hukumar Batsari, ya tuna da yadda aka yi watsi da kauyen da ke dauke dumbin mutane, kuma wannan hare-hare na ‘yan ta’adda ke faruwa a cikinsa.
“Na tuna da wani mummunan al’amari da ya faru ranar Talata, inda mahara suka kai farmaki kauyenmu da misalign karfe hudu na yamma, inda suka yi ta faman harbe-harbe babu kakkautawa tare da tilastawa mazauna garin yin hijira. A wannan rana, wasu mata sun haihu yayin da suke gudu, don tseratar da rayuwarsu, wasu kuma suka yi bari.

Kazalika, haka yara suka rika gudu babu takalmi a kafarsu zuwa garin Batsari, don neman mafaka”, in ji shi.

Aliyu ya kara da cewa, an yi garkuwa da mutanen kauyen da dama, domin samun kudin fansa, yayin da wasu kuma suka rasa rayukansu a hare-haren.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Next Post
Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan

Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.