• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sulhun Shugabannin Al’umma Da ‘Yan Bindiga Ke Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

by Sani Anwar and Sulaiman
4 months ago
in Labarai
0
Kawayen amarya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabannin al’umma a Kananan Hukumomin Jibiya, Batsari da Safana na Jihar Katsina, sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan bindigar da ke addabar kauyukansu.

Mazauna yankin sun ce, an yi zaman sulhun a baya-bayan nan tsakanin Shugabannin Karamar Hukumar Jibiya da ‘yan ta’adda a ranar Juma’a 28 ga watan Fabrairu, biyo bayan irin wannan yarjejeniyoyin da aka yi a Kananan Hukumomin Batsari da Safana, wadanda suka sha fama da hare-hare babu kakkautawa saboda kusancinsu da Dajin Rugga.

  • Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 
  • NPA Za Ta Yunkuro Don Zamanantar Da Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya – Dantsoho

Har ila yau, kamar yadda suka bayyana; tattaunawar ta samu halartar wakilan sojoji, jami’an tsaron farin kaya (DSS), ‘yansanda, jami’an sa ido na al’umma, ‘yan banga, sarakunan gargajiya da jami’an kananan hukumomi.

Kazalika, an bayyana cewa; wani sanannen shugaban ‘yan bindiga a yankin, Audu Lankai ne ya kaddamar da yarjejeniyar, inda ya nuna takaicinsa kan yadda rikicin ya dade ana yin sa.

Wata majiya mai tushe a Jibiya ta ce, “Babu hannun gwamanatin jihar kai tsaye a sulhun, domin kuwa gwamnan ya sha nanata cewa; ba zai tattauna da ‘yan bindiga ba, matukar ba su mika wuya sakamakon matsin lamba ba.”

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

“Amma a wannan karon, shugabannin al’ummarmu; sun gana da daya daga cikin manyan jami’an gwamnati, sannan sun ba mu goyon bayansu, bisa la’akari da halin da muke ciki.

Shugaban ‘yan bindigar Audu Lankai ne ya bukaci zaman wannan sulhu tare da bayyana cewa; ya gaji da wadannan tashe-tashen hankula da suke faruwa.

“Ya tuntubi daya daga cikin shugabanninmu, bayan tattaunawa mai tsawo, mun kuma amince da haduwa ranar Juma’a. Kazalika, mun amince da ci gaba da tattaunar zaman lafiya bayan Sallah, idan dukkanin bangarorin biyu suka mutunta sharuddan yarjejeniyar.”
Sharuddan da al’ummar Jibiya suka gindaya, sun hada da dakatar da hare-haren da ake kai wa matafiya a kan titin Jibiya zuwa Katsina, Batsari zuwa Batsari da kuma Jibia zuwa Gurbi da kuma kawo karshen hare-haren da ake kai wa kauyuka da garkuwa da mutane, barin manoma da mazauna yankunansu ci gaba da ayyukansu da sakin wadanda aka kama da kuma ajiye makamai.

Ya kara da cewa, ya zuwa yanzu an kubutar da mutum 11 da aka yi garkuwa da su, sannan ‘yan bindigar sun mika makamai biyu.

Majiyar ta kuma ce, ‘yan bindigar sun bukaci a bai wa ‘yan ta’addar damar shiga cikin al’umma, ba tare da wata barazana ga rayuwarsu ba, saboda bukatar kare kai daga kungiyoyin da ke gaba da juna da kuma wadanda ba ‘yan ta’adda ba.

A cikin wani faifan bidiyo, wani dan bindiga mai suna Bala Wuta, ya yi jawabi a makarantar firamare ta Kwari, inda ya koka da irin asarar da aka samu daga bangarorin biyu.

Ya bukaci gwamnati ta samar da ababen more rayuwa da suka hada da makarantu, wuraren ruwan sha da magunguna ga makiyaya, domin samun fahimtar juna.

Wani daga cikin shugabannin al’umma a Jibiya da bukaci a sake sunansa, ya tabbatar da yarjejeniyar zaman lafiyar, inda ya ce; “Hatta Annabi Muhammad SAW, ya shiga yarjejeniyar zaman lafiya, ma’ana wannan wani abu ne da Allah ya yarda da shi, domin kuwa; babu wata fa’ida a cikin rikici, idan bangarorin biyu na son kawo karshensa.

 

Zaman Lafiya Ya Fi Komai Dadi- Mazauna Kauyukan

Mazauna kauyukan da al’amarin ya shafa, sun bayyana jin dadinsu, inda suka bayyana cewa; shirin samar da zaman lafiyar da al’umma ke yi ya fara nuna kyakkyawan sakamako.

Haka zalika, sun bayyana cewa; yankunan da ake gani sun fi hatsarin ziyarta, sannu a hankali ana samun dawowar zaman lafiya na rayuwar yau da kullum.

Malam Yahuza Aliyu, Mataimakin Hakimin Kauyen Wagini a Karamar Hukumar Batsari, ya tuna da yadda aka yi watsi da kauyen da ke dauke dumbin mutane, kuma wannan hare-hare na ‘yan ta’adda ke faruwa a cikinsa.
“Na tuna da wani mummunan al’amari da ya faru ranar Talata, inda mahara suka kai farmaki kauyenmu da misalign karfe hudu na yamma, inda suka yi ta faman harbe-harbe babu kakkautawa tare da tilastawa mazauna garin yin hijira. A wannan rana, wasu mata sun haihu yayin da suke gudu, don tseratar da rayuwarsu, wasu kuma suka yi bari.

Kazalika, haka yara suka rika gudu babu takalmi a kafarsu zuwa garin Batsari, don neman mafaka”, in ji shi.

Aliyu ya kara da cewa, an yi garkuwa da mutanen kauyen da dama, domin samun kudin fansa, yayin da wasu kuma suka rasa rayukansu a hare-haren.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Cire Haraji Ya Sa Albashinmu Babu Albarka – SSANU

Next Post

Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

5 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

5 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

6 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

6 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

9 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

10 hours ago
Next Post
Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan

Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.