• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu

by CMG Hausa
2 years ago
Kasar Sin

A tsakiyar makon nan ne mahukuntan kasar Sin suka mikawa gwamnatin Zimbabwe tallafin gaggawa na kayan abinci, wadanda za a rabawa rukunin mabukata a kasar, wadanda suka hada da mutane masu bukata ta musamman da sauran masu rauni.

Ko shakka babu, wannan tallafi da ya kushi tan 1,000 na shinkafa, da tan 1,000 na alkama, zai yi matukar agazawa masu rauni dake Zimbabwe ta fannin samun isasshiyar cimaka, wanda hakan manufa ce ta bai daya tsakanin Sin da Zimbabwe a bangaren wadatar da al’ummun su da abinci.

  • Gidan Yari Da Ya Saba Doka Da Amurka Ta Kafa Misali Ne Na Take Hakkin Doka Da ‘Yancin Dan Adam

Kaza lika, masharhanta na ganin tallafi na Sin a matsayin shaida dake tabbatar da karkon kawancen gargajiya dake tsakanin kasashen biyu.

Ba dai wannan ne karon farko da Zimbabwe, da ma karin wasu kasashen Afirka da dama ke karbar makamancin wannan tallafi daga bangaren kasar Sin ba, wanda hakan ke nuni da cewa, yayin Sin ke samun karin bunkasar tattalin arziki da wadata, a hannu guda ba ta manta da ’yan uwan ta kasashe masu tasowa dake cikin yanayi na bukata ba.

Tuni dai mahukuntan Sin suka cika alkawura masu yawa da suka dauka na bunkasa hadin gwiwa da kasashen Afirka, ciki har da kasar Zimbabwe, kasar da ba ya ga irin wadannan tallafin gaggawa da ta samu daga Sin har karo 10 tsakanin shekarar 2002 zuwa yanzu, ta kuma ci gajiyar agajin bunkasa tattalin arziki, da raya ababen more rayuwa, irin su haka rijiyoyin birtsatsai a yankunan karkararta, da kafa cibiyar gwajin dabarun noma, da madatsun ruwa, da filayen noman rani, da sauran shirye-shiryen hadin gwiwar raya noma da Sin din ke jagoranta. Har ila yau, Zimbabwe ta mori shirye-shiryen tallafawa fannin kiwon lafiya, da ilimi da bunkasa zamantakewar al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

A daya bangaren kuma, kasar Sin tana ci gaba da dora muhimmanci ga tallafawa Zimbabwe da dabarun inganta noma, ta hanyar samar mata da na’urorin aiki na zamani, da bunkasa kwarewa da zuba jari.

La’akari da wannan, da ma sauran fannonin raya ci gaba da Zimbabwe ke mora daga Sin, ya sa mahukuntan kasar ke jinjinawa Sin, tare da kara amincewa da ita a matsayin kawa ta hakika ga ita kanta Zimbabwe din da ma sauran kasashen nahiyar Afirka. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11
Daga Birnin Sin

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera
Daga Birnin Sin

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
Next Post
Dakarun Soji  4 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Bauchi

Mutane 11 Sun Rasu, 8 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Edo

LABARAI MASU NASABA

Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.