• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A tsakiyar makon nan ne mahukuntan kasar Sin suka mikawa gwamnatin Zimbabwe tallafin gaggawa na kayan abinci, wadanda za a rabawa rukunin mabukata a kasar, wadanda suka hada da mutane masu bukata ta musamman da sauran masu rauni.

Ko shakka babu, wannan tallafi da ya kushi tan 1,000 na shinkafa, da tan 1,000 na alkama, zai yi matukar agazawa masu rauni dake Zimbabwe ta fannin samun isasshiyar cimaka, wanda hakan manufa ce ta bai daya tsakanin Sin da Zimbabwe a bangaren wadatar da al’ummun su da abinci.

  • Gidan Yari Da Ya Saba Doka Da Amurka Ta Kafa Misali Ne Na Take Hakkin Doka Da ‘Yancin Dan Adam

Kaza lika, masharhanta na ganin tallafi na Sin a matsayin shaida dake tabbatar da karkon kawancen gargajiya dake tsakanin kasashen biyu.

Ba dai wannan ne karon farko da Zimbabwe, da ma karin wasu kasashen Afirka da dama ke karbar makamancin wannan tallafi daga bangaren kasar Sin ba, wanda hakan ke nuni da cewa, yayin Sin ke samun karin bunkasar tattalin arziki da wadata, a hannu guda ba ta manta da ’yan uwan ta kasashe masu tasowa dake cikin yanayi na bukata ba.

Tuni dai mahukuntan Sin suka cika alkawura masu yawa da suka dauka na bunkasa hadin gwiwa da kasashen Afirka, ciki har da kasar Zimbabwe, kasar da ba ya ga irin wadannan tallafin gaggawa da ta samu daga Sin har karo 10 tsakanin shekarar 2002 zuwa yanzu, ta kuma ci gajiyar agajin bunkasa tattalin arziki, da raya ababen more rayuwa, irin su haka rijiyoyin birtsatsai a yankunan karkararta, da kafa cibiyar gwajin dabarun noma, da madatsun ruwa, da filayen noman rani, da sauran shirye-shiryen hadin gwiwar raya noma da Sin din ke jagoranta. Har ila yau, Zimbabwe ta mori shirye-shiryen tallafawa fannin kiwon lafiya, da ilimi da bunkasa zamantakewar al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

A daya bangaren kuma, kasar Sin tana ci gaba da dora muhimmanci ga tallafawa Zimbabwe da dabarun inganta noma, ta hanyar samar mata da na’urorin aiki na zamani, da bunkasa kwarewa da zuba jari.

La’akari da wannan, da ma sauran fannonin raya ci gaba da Zimbabwe ke mora daga Sin, ya sa mahukuntan kasar ke jinjinawa Sin, tare da kara amincewa da ita a matsayin kawa ta hakika ga ita kanta Zimbabwe din da ma sauran kasashen nahiyar Afirka. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Next Post

Mutane 11 Sun Rasu, 8 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Edo

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

6 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

8 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

9 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

10 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

1 day ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

1 day ago
Next Post
Dakarun Soji  4 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Bauchi

Mutane 11 Sun Rasu, 8 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Edo

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.