• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tallafin Gaggawa Da Kasar Sin Ta Samarwa Zimbabwe Ya Kara Fito Da Manufar Kawancen Gargajiya Tsakanin Sassan Biyu

by CMG Hausa
2 years ago
Kasar Sin

A tsakiyar makon nan ne mahukuntan kasar Sin suka mikawa gwamnatin Zimbabwe tallafin gaggawa na kayan abinci, wadanda za a rabawa rukunin mabukata a kasar, wadanda suka hada da mutane masu bukata ta musamman da sauran masu rauni.

Ko shakka babu, wannan tallafi da ya kushi tan 1,000 na shinkafa, da tan 1,000 na alkama, zai yi matukar agazawa masu rauni dake Zimbabwe ta fannin samun isasshiyar cimaka, wanda hakan manufa ce ta bai daya tsakanin Sin da Zimbabwe a bangaren wadatar da al’ummun su da abinci.

  • Gidan Yari Da Ya Saba Doka Da Amurka Ta Kafa Misali Ne Na Take Hakkin Doka Da ‘Yancin Dan Adam

Kaza lika, masharhanta na ganin tallafi na Sin a matsayin shaida dake tabbatar da karkon kawancen gargajiya dake tsakanin kasashen biyu.

Ba dai wannan ne karon farko da Zimbabwe, da ma karin wasu kasashen Afirka da dama ke karbar makamancin wannan tallafi daga bangaren kasar Sin ba, wanda hakan ke nuni da cewa, yayin Sin ke samun karin bunkasar tattalin arziki da wadata, a hannu guda ba ta manta da ’yan uwan ta kasashe masu tasowa dake cikin yanayi na bukata ba.

Tuni dai mahukuntan Sin suka cika alkawura masu yawa da suka dauka na bunkasa hadin gwiwa da kasashen Afirka, ciki har da kasar Zimbabwe, kasar da ba ya ga irin wadannan tallafin gaggawa da ta samu daga Sin har karo 10 tsakanin shekarar 2002 zuwa yanzu, ta kuma ci gajiyar agajin bunkasa tattalin arziki, da raya ababen more rayuwa, irin su haka rijiyoyin birtsatsai a yankunan karkararta, da kafa cibiyar gwajin dabarun noma, da madatsun ruwa, da filayen noman rani, da sauran shirye-shiryen hadin gwiwar raya noma da Sin din ke jagoranta. Har ila yau, Zimbabwe ta mori shirye-shiryen tallafawa fannin kiwon lafiya, da ilimi da bunkasa zamantakewar al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

A daya bangaren kuma, kasar Sin tana ci gaba da dora muhimmanci ga tallafawa Zimbabwe da dabarun inganta noma, ta hanyar samar mata da na’urorin aiki na zamani, da bunkasa kwarewa da zuba jari.

La’akari da wannan, da ma sauran fannonin raya ci gaba da Zimbabwe ke mora daga Sin, ya sa mahukuntan kasar ke jinjinawa Sin, tare da kara amincewa da ita a matsayin kawa ta hakika ga ita kanta Zimbabwe din da ma sauran kasashen nahiyar Afirka. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Next Post
Dakarun Soji  4 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Bauchi

Mutane 11 Sun Rasu, 8 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Edo

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.