• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tasirin Sauyin Yanayi Ke Shafar Yankuna A Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
1 year ago
in Labarai
0
Yadda Tasirin Sauyin Yanayi Ke Shafar Yankuna A Jihar Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahoton da Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya ta fitar a 2019 ya bayyana cewa Nijeriya ta na asarar kimanin fili mai fadin murabba’in kadada 350,000 a duk shekara, sakamakon yadda hamada ke ci gaba da mamayewar yankuna, wanda hakan ya na faruwa ne ta musababbin sauyin yanayi, mai alaka da ayyukan yau da kullum da Dan Adam masu jawo dumamar yanayi.

A nata bangaren, a wani sabon binciken da Hukumar Agora Policy ta gudanar a wannan shekara (2023), ta bayyana cewa, Nijeriya zata iya yin hasarar Dalar Amurka kimanin biliyan 460 sakamakon sauyin yanayin da duniya ke fuskanta, nan da shekarar 2050 mai zuwa, matukar ba ta dauki ingantattun matakan kan-da-garki ba.

  • Akidar Siyasar Malam Aminu Kano Da Ta ‘Yan Siyasar Yanzu A Mizani –Farfesa Habu
  • Sojojin Ruwan Kasar Sin Sun Shafe Shekaru 15 Suna Aikin Tabbatar Da Tsaro A Mashigin Tekun Aden Da Gabar Tekun Somaliya

Jihar Yobe ta na daya daga cikin Nijeriya masu fuskantar matsalolin gurgusowar hamada mai alaka da sauyin yanayi, al’amarin da yake da alaka da sha’anin tsarin tattalin arziki, zamantakewa da al’adu, wanda ya dace a samu sauyin da za su taimaka wajen rage dumamar yanayin da canjinsa. Haka kuma, sakamakon tasirin sauyin yanayin ya na shafar yankuna da al’ummar jihar kai-tsaye, wanda yake zama babbar barazana ga ci gaba da yanayin rayuwar mazauna yankunan.

Bugu da kari kuma, yankunan kananan hukumomin Yunusari, Yusufari, Geidam, Bade, Karasuwa, Machina, Bursari, da Tarmuwa a jihar Yobe, su na daga cikin sassan jihar wadanda suke dandana kudarsu a hannun sauyin yanayin, kuma babbar barazana ga mazauna yankunan.

LEADERSHIP Hausa ta jiyo ta bakin Mallam Baba Alkali, Sakataren karamar hukumar Yusufari, a jihar Yobe, ya bayyana cewa sakamakon sauyin yanayin, yankunansu na fuskantar karancin ruwan sama, sabanin shekarun baya, wanda ya jawo tankardar noma da abinci ga al’ummar yankin.

Labarai Masu Nasaba

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

A nashi bangaren, Lawanin kauyen Gremadi, Alhaji Maidala Zanna, ya ce hata mafi yawan hanyoyin su na mota zuwa kauyukansu rairayin hamadar ya mamaye, wanda hakan ya sanya ba kowace mota za ta shiga kauyukan ba.

‘’Mamayar yashin hamadar ya yi tsanani fiye da kowane lokaci a sanin da muka yi, saboda a shekarun baya rairayi ya mamaye kashi 10 ne cikin dari na gonakinmu, amma yanzu ya bar mana 40 ne kawai muke iya shuka amfanin gona, sauran kashi 60 din duk yashi ne ya nutsar dasu.”

Ya ce, “A cikin wannan kashi 40 cikin dari, kashi 25 ne kawai na noman amfanin gona, kashi 15 kuma na kiwon dabbobi ne, amma ko wannan fili da muka bar shi don kiwo, wasu Fulani daga jamhuriyar Nijar sun mamaye shi don kiwon dabbobinsu kuma sun hanamu sakat a matsayinmu na yan kasa. Shima wannan wani babban kalubale ne garemu.”

“Wannan kakkarfar guguwar mai dauke da dusar kura ta na ci gaba da mamaye wa da lalata gidajenmu masu yawan gaske a yankunanmu. Haka kuma, yanzu haka da nake magana da ku katangar gidana ta rushe a karo na uku, sakamakon wannan bala’i na zaizayar hamada.”

Wakilinmu ya lura da cewa sakamakon dumamar yanayi da sauyin yanayi, guguwar yashi da kura sun ribanya, al’amarin da ya jawo karancin ruwan sama a wannan yankin, inda ya janyo farin da ake samun hatsaniya tsananin makiyaya da manoma a duk shekara.

Malam Ahmed Abubakar masani kan sauyin yanayi, ya ce jihar Yobe na daya daga cikin jahohin da ke kan gaba, wadanda ke makwabtaka da jamhuriyar Nijar, masu fuskantar kalubalen gurgusowar hamada sakamakon iskar kasurwar arewa maso gabas mai karfin gaske.

Ya kara da cewa, ‘’Yobe ta na cikin Jihohi 19 da ke kan gaba kan matsalolin gurgusowar hamada masu iyaka da Jamhuriyar Nijar, yanki ne wanda yake kan gaba a hamadar Sahara.”

“Sannnan kuma a koda yaushe al’amarin ya na yin tasiri ne sakamakon wannan sauyin yanayi wanda ya hada da iska mai dauke da kura mai gusar da rairayi, sakamakon guguwar da ke tasowa daga kasurwar Arewa Maso Gabas.”

‘’Don haka duk lokacin da wannan iskar ke tasowa ta wuce a kusan watan Nuwamba zuwa Maris a kowace shekara, muna fuskantar matsalar kura mai karfin gaske, ta na haifar da gurgusowar hamada a gurare da dama tare da kawo matsaloli daban-daban ga yankuna tare da al’ummar wadannan yankuna.”

Ya ce, mafita daya wadda ta dace wajen magance wannan matsala, ita ce dashen itace masu yawa a kowane lungu da sako. Ya ce, dalilin da ya sa gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani shirin dashen itatuwa na ‘Great Green Wall’ wanda shirin ya na da nufin gina katafariyar gandun bishiyoyi a kowane bangare na kasar nan. Wanda shi ne zai bai wa muhallinmu kariya daga mummunar illar gurgusowar hamada.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankin Raya Afirka Ya Bukaci Nijeriya Ta Kawo Karshen Cin Bashi

Next Post

Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

Related

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri
Labarai

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

12 minutes ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

1 hour ago
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
Labarai

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

3 hours ago
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
Labarai

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

4 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

12 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

13 hours ago
Next Post
Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.