Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki a yankin Kugauta da ke Kusheka, da kuma Kitanda da ke Geshere a karamar hukumar Kauru ta jihar Kaduna tare da yin garkuwa da mutane 22.
Wani Dalibin Majami’a kuma mazaunin garin Emmanuel Johnson, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wata hira da manema labarai ta wayar tarho a Kaduna, ya ce ‘yan bindigar sun mamaye al’ummomin biyu ne a wasu hare-hare a daren Juma’a da misalin karfe 10:30 na dare, inda suka yi garkuwa da mutanen wanda mafi yawancinsu mata da kananan yara ne.
- Rikicin Ƙabilanci Da Saɓanin Makiyaya Da Manoma Ya Zama Tarihi A Jihar Kaduna – KSPC
- Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Bindigar Tankar Mai A Enugu
Ya tabbatar da cewa, an yi garkuwa da mutanen 12 a yankin Kitanda da ke Geshere, yayin da wasu 10 kuma aka yi garkuwa da su daga yankin Kugauta na Kusheka.
Ba a samu jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Kaduna (PPRO), DSP Mansir Hassan ba da aka tuntube shi har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp