• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Haraji Da Gwamnatin Amurka Ke Gudanarwa Na Jefa Fargaba a Zukatan Amurkawa

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yakin Haraji Da Gwamnatin Amurka Ke Gudanarwa Na Jefa Fargaba a Zukatan Amurkawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Amurkawa na kara damuwa game da yakin haraji da gwamnatinsu ke gudanarwa a sabon zagaye albarkacin kusantowar kafuwar sabuwar gwamnatin kasar. A watan Disamba na shekarar bara, wani bincike da aka yi, bisa jin ra’ayin Amurkawa 2000, sulusinsu na cike da matukar tsoro, da damuwa game da manufar harajin da sabuwar gwamnatin kasar za ta aiwatar a nan gaba.

Yawan sayayya fiye da kima, da adana hajoji a cikin gida da Amurkawa suke yi bai zo da mamaki ba, duba da cewa, bisa wasu binciken da aka yi, matsin lamba da batun haraji ke haifarwa na damun Amurkawa masu sayayya. Kazalika kara buga haraji kan hajojin dake shiga kasar ya haifar da hauhawar farashi da ya kai kaso 10% a wani lokaci.

  • Xi Ya Zanta Da Babban Jagoran Vietnam Da Shugaban Sri Lanka
  • Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS

Daya daga cikin dalilan da gwamnatin Amurka ke cewa ya sa ta aiwatar da manufar harajin shi ne burin dawo da masana’antun samar da kayayyaki cikin gida. To sai dai kuma sakamakon da aka samu ya saba da hakan. Zai fi kyau a yi tunani mai zurfi kan matsalolin da tattalin arzikin Amurka ke fuskanta, a maimakon raya masana’antar samar da kayayyaki ta hanyar aiwatar da manufar haraji.

Bari mu duba bangaren samar da guraben aikin yi. Wannan manufa ta ba da kariya ga wasu sana’o’i, amma a daya hannun, matakin da wasu kasashe suka dauka na martani, ya haifar da raguwar ribar kamfanonin Amurka, da ma tsagaita ajandar karuwar albashi, da shirin habakar kamfanonin kasar, da ma illata halin samar da guraben aikin yi.

Gwamnatin Amurka na amfani da haraji wajen cimma burinta na siyasa, amma matakin ba zai hana bunkasuwar Sin ba ko kadan, kuma ba zai haifar da jinkirin zuba jarin kamfanonin kasar a kasar Sin ba.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Gwamnatin Sin ta fitar da alkaluma dake cewa, a shekarar bara, yawan hajojin da Sin ta yi shige da ficensu ya kai sabon matsayi a tarihi, yayin da cinikin shige da fice na Sin ya kai matsayin farko a duniya a cikin shekaru 8 a jere. Har illa yau, Amurkawa sun kafa kamfanoni fiye da dubu 73 a Sin, kana yawan kudin da suka zuba a Sin ya kai fiye da dala triliyan 1.2.

Cimma nasarori tare tsakanin bangaren Sin da Amurka, zarafi ne ga saura a maimakon kalubale, don haka ya kamata sun yi hakuri da juna, su samu ci gaba da wadata irin nasu, domin kaucewa dandana bacin rai sakamakon yakin haraji da ciniki. (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hamas Ta Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Isra’ila

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Harbi Likita Tare Da Garkuwa Da Ma’aikatan Jinya A Wani Harin Asibiti A Katsina

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

15 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

18 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

21 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

22 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

23 hours ago
Next Post
Kawayen amarya

'Yan Bindiga Sun Harbi Likita Tare Da Garkuwa Da Ma'aikatan Jinya A Wani Harin Asibiti A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.