• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Haraji Da Gwamnatin Amurka Ke Gudanarwa Na Jefa Fargaba a Zukatan Amurkawa

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yakin Haraji Da Gwamnatin Amurka Ke Gudanarwa Na Jefa Fargaba a Zukatan Amurkawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Amurkawa na kara damuwa game da yakin haraji da gwamnatinsu ke gudanarwa a sabon zagaye albarkacin kusantowar kafuwar sabuwar gwamnatin kasar. A watan Disamba na shekarar bara, wani bincike da aka yi, bisa jin ra’ayin Amurkawa 2000, sulusinsu na cike da matukar tsoro, da damuwa game da manufar harajin da sabuwar gwamnatin kasar za ta aiwatar a nan gaba.

Yawan sayayya fiye da kima, da adana hajoji a cikin gida da Amurkawa suke yi bai zo da mamaki ba, duba da cewa, bisa wasu binciken da aka yi, matsin lamba da batun haraji ke haifarwa na damun Amurkawa masu sayayya. Kazalika kara buga haraji kan hajojin dake shiga kasar ya haifar da hauhawar farashi da ya kai kaso 10% a wani lokaci.

  • Xi Ya Zanta Da Babban Jagoran Vietnam Da Shugaban Sri Lanka
  • Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS

Daya daga cikin dalilan da gwamnatin Amurka ke cewa ya sa ta aiwatar da manufar harajin shi ne burin dawo da masana’antun samar da kayayyaki cikin gida. To sai dai kuma sakamakon da aka samu ya saba da hakan. Zai fi kyau a yi tunani mai zurfi kan matsalolin da tattalin arzikin Amurka ke fuskanta, a maimakon raya masana’antar samar da kayayyaki ta hanyar aiwatar da manufar haraji.

Bari mu duba bangaren samar da guraben aikin yi. Wannan manufa ta ba da kariya ga wasu sana’o’i, amma a daya hannun, matakin da wasu kasashe suka dauka na martani, ya haifar da raguwar ribar kamfanonin Amurka, da ma tsagaita ajandar karuwar albashi, da shirin habakar kamfanonin kasar, da ma illata halin samar da guraben aikin yi.

Gwamnatin Amurka na amfani da haraji wajen cimma burinta na siyasa, amma matakin ba zai hana bunkasuwar Sin ba ko kadan, kuma ba zai haifar da jinkirin zuba jarin kamfanonin kasar a kasar Sin ba.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Gwamnatin Sin ta fitar da alkaluma dake cewa, a shekarar bara, yawan hajojin da Sin ta yi shige da ficensu ya kai sabon matsayi a tarihi, yayin da cinikin shige da fice na Sin ya kai matsayin farko a duniya a cikin shekaru 8 a jere. Har illa yau, Amurkawa sun kafa kamfanoni fiye da dubu 73 a Sin, kana yawan kudin da suka zuba a Sin ya kai fiye da dala triliyan 1.2.

Cimma nasarori tare tsakanin bangaren Sin da Amurka, zarafi ne ga saura a maimakon kalubale, don haka ya kamata sun yi hakuri da juna, su samu ci gaba da wadata irin nasu, domin kaucewa dandana bacin rai sakamakon yakin haraji da ciniki. (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hamas Ta Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Isra’ila

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Harbi Likita Tare Da Garkuwa Da Ma’aikatan Jinya A Wani Harin Asibiti A Katsina

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

18 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

19 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

20 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

21 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

22 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

23 hours ago
Next Post
Kawayen amarya

'Yan Bindiga Sun Harbi Likita Tare Da Garkuwa Da Ma'aikatan Jinya A Wani Harin Asibiti A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.