• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Adawa Na Kitsa Makarkashiyar Tsige Ni – Akpabio

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
3 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya, Manyan Labarai
0
Akpabio
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Obot Akpabio, ya bayyana cewa wasu ‘yan siyasa daga jihohin Adamawa da Kwara da ke jam’iyyun adawa na kitsa makarkashiyar tsige shi daga mukaminsa.

Ya bayyana hakan ne lokacin da ya amshi bakoncin shugabannin kungiyoyin matasan Neja Dalta a Abuja.

  • Mutane 7 Sun Mutu, Kadarorin Miliyan 50.3 Sun Salwanta Dalilin Gobara A Kano
  • Wata Rana Za A Yi Wa Gwamnatin Tinubu Sambarka – Minista 

Ko da yake bai ambaci sunaye ba, amma maganar ta yi nuni ga tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da kuma tsohon shugaban majalisar dattawa, Abubakar Bukola Saraki wadanda suka fito daga Adamawa da Kwara, kuma a kwanakin baya ne suka fitar da sanarwar ya sauka daga shugabancin majalisar dattawa sakamakon lamarin da ya janyo cece-kuce tsakaninsa da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

Duk da sun san cewa dokokin majalisar dattawan da suka shafi rashin da’a, Akpabio ya koka da cewa mutanen da ake magana da su suna yin watsi da hakikanin al’amuran da gangan saboda siyasar adawa.

“Don haka lokacin da mutane suka hada kai, sai na ji muryoyi daga Adamawa da Kwara suna ihu,ana amfani da wasu matasa daga yankin kudu maso yamma wajen yin adawa ta siyasa.Ya kamata mutum ya dunga tauna magana kafin ya fade ta”, n ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Da yake jaddada cewa ya kamata mutane su fahimci cewa a matsayinsa na shugaban majalisar dattawa, ba wai shi kadai ke wakiltar mazabarsa da jam’iyyarsa ba, har ma da yankin da ba a taba rike wannan mukami ba tsawon shekaru 46 da suka gabata.Shugaban majalisar ya bukaci wadanda ke sukar sa da su yi shiru da bakinsu.

Akpabio ya bayyana cewa shugaban majalisar dattawa ba wai kansa kadai yake wakiltar ba, al’ummar yankin Neja Delta gaba daya ba yake wakilta.

A yayin da yake jawabi a kan batun samar da kujerun zama da ya shafi Natasha Akpoti-Oduaghan, wanda ya kai ga zargin cin zarafi, Shugaban Majalisar Dattawan ya jaddada cewa mutane suna ihu ne kawai ba tare da fahimtar ka’idojin da aka shimfida ba na majalisar dattawa.

Ya ce wadanda ba su san ayyukan cikin gida na majalisar dokoki ta kasa ba za su iya fahimtar abin da ya kai ga dakatar da Natasha ba.

Da yake kare matakin dakatarwar da aka yi wa Natasha Akpoti-Uduaghan na tsawon watanni shida, Akpabio ya bayyana cewa, matakin bai daya ne na daukacin majalisar ba tare da ko daya daga cikin ‘yan majalisa da ya nuna adawa da shi ba.

Shugaban majalisar ya bukace masu sukar da su daina yin sharhin da ba su sani ba game da majalisar.

Tun da farko, Shugaban Majalisar Matasan Ijaw,Jonathan Lokpobiri wanda ya jagoranci tawagar ya nuna damuwarsa game da abubuwan da ke faruwa a majalisar dattawa, ya kuma tabbatar wa Akpabio cewa mutanen Neja Delta suna mara masa baya.

Lokpobiri ya kuma nemi shugaban majalisar dattawan ya sa baki kan rikicin da ke kunno kai a Jihar Ribas, yana mai gargadin cewa za ta iya nausawa har zuwa yankin Neja Delta baki daya idan ba a yi la’akari da shi ba.

Game da yanayin da ya shafi Natasha, shugaban matasan ya nuna damuwarsu, ko da ya ce ya kamata a dauki lamarin a matsayin batun cikin gida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashford Ya Koma Tawagar Ingila Bayan Shekara Ɗaya

Next Post

Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

57 minutes ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

15 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba

Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba

LABARAI MASU NASABA

Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.