Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton a karkashin Bello Turji wanda ake nema ruwa a jallo suke, sun kashe mutane 12 a garin Lugu da ke karamar hukumar Isa ta jihar Sokoto.
Majiyoyi sun shaida wa LEADERSHIP a ranar Alhamis cewa, an kai harin ne a lokacin da ’yan bindigar ke dawowa daga ziyarar Sallah a daya daga cikin al’ummar karamar hukumar Isa, inda suka harbe manoman.
- Nasara A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda: Tattalin Arziƙin Jihar Zamfara Na Ƙara Haɓaka – Gwamna Lawal
- Trump Ya Ƙaƙaba Wa Nijeriya Da Ƙasashen Duniya Haraji
Dan majalisa mai wakiltar Sabon Birni a majalisar dokokin jihar, Hon. Aminu Boza, ya ce wasu mutanen yankin ne suka sanar da shi harin, amma babu labarin cewa Turji ya ziyarci wata al’umma a mazabarsa domin yin bikin Sallah.
Ya ce, “Akwai rahoton cewa Turji ya shirya zai ziyarci yankin Gabashin Gatawa domin gudanar da bukukuwan Sallah, amma matakin da jama’a suka dauka na sanar da jami’an tsaro ya dakatar da shi ga hakan.
“Wannan na iya zama dalilin da ya sa Bello Turji ya huce fushinsa a kan manoman da ba su ji ba gani ba.”
Sai dai hukumomin ‘yansanda a jihar sun ki cewa komai kan lamarin.
Majiyar ‘yansandan ta yi ikirarin cewa, “tunda ana ci gaba da aikin hadin gwiwa na sojoji a yankin, ‘yansanda ba su da hurumin yin magana kan ci gaban tsaro a yankin.
Da aka tuntubi runduna ta 8 ta sojojin Nijeriya ta mika wakilinmu ga rundunar ‘Operation FASAN YAMMA’, wanda har yanzu bai amsa bukatar wakilinmu ba kan bukatar tabbatar da lamarin harin har zuwa lokacin rubuta wannan rahoton.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp