ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Farmaki Hadimin Gwamnan Bauchi, Sun Jikkata Mutum 1

by Khalid Idris Doya
3 years ago
'Yansanda

Wasu ‘yan bindigan da ba a gano ko su waye ba zuwa yanzu sun kai hari gidan babban mai taimaka wa gwamnan Jihar Bauchi kan harkokin kula da Kiristoci, Fasto Zakka Luka Magaji a gidansa da ke kauyen Birshi da ke cikin garin Bauchi.

‘Yan bindigan da yawansu ya kai bakwai sun mamaye gidan Luka ne da kokarin yin garkuwa da shi ko barazana ga rayuwarsa. Amma cikin ikon Allah basu samu nasarar hakan ba 

  • Kamfanonin Kasar Sin Sun Shirya Taron Horar Da Matasan Afrika
  • Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

A lokacin harin, wani matashi mai shekara 32 da ya kasance mambar cocin Christian Life da ke zaune tare da Fasto Zakka din an jikkata shi.

ADVERTISEMENT

A lokacin da kwamishinan kula da harkokin addinai na jihar Bauchi, Hon Umar Babayo Kesa ya jagoranci tawagar ma’aikatarsa don kai ziyarar jaje ga Faston, Zakka ya shaida cewa ba su san dalilin wadanda suka kawo masa harin ba, “Amma cikin ikon Allah, Allah ya karemu. Kuma wadda ya jikkatan zuwa yanzu yana samun sauki.”

A nasa fannin, Umar Babayo Kesa, ya shaida cewar sun zo ne domin jajanta wa Faston bisa wannan harin da aka kai masa. 

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Ya yi addu’ar Allah ya cigaba kare shi da iyalansa daga hannun miyagun. 

Faston ya gode musu bisa wannan ziyarar ya nuna hakan a matsayin matakin da zai Kara kyautata zaman lafiya a tsakanin al’ummar jihar.

Ita ma rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, ta tabbatar da faruwar lamarin ta bakin kakakinta, Ahmed Wakil, inda ya ce tunin aka fara kokarin cafko maharan.

Ya ce, rundunar ta samu kiran waya kan lamarin wajajen karfe 0013hrs inda suka dauki matakin tura jami’ai da kai daukin gaggawa.

Ya ce lokacin da jami’an ‘yansandan suka isa wajen, sun samu kwanson harsasai uku samfurin 7.6mm.

Wakil ya kara da cewa sun dauki wadda aka jikkata zuwa asibitin ATBUTH domin kulawar Likitoci  

Ya cigaba da cewa suna kokarin daukan matakan da suka dace domin cafko wadanda suka kai wannan harin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
FBI Na Neman Wani Dan Nijeriya Da Ya Damfari Amurka Dala Miliyan 30

FBI Na Neman Wani Dan Nijeriya Da Ya Damfari Amurka Dala Miliyan 30

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.