• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Jarida Sun Cancanci Samun Rayuwa Mai Inganci A Nijeriya – Minista

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Jarida Sun Cancanci Samun Rayuwa Mai Inganci A Nijeriya – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ‘yan jarida a Nijeriya suna aiki a cikin mawuyacin yanayi, kuma sun cancanci samun ingantacciyar rayuwa, yadda za su samu damar gudanar da ayyukansu cikin sauki da walwala.

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris ne, ya bayyana haka a wata tattaunawa da ya yi da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), a Abuja.

  • Kada Ku Bari ‘Yan Bindiga Su Shafe Baki Daya – Baraje
  • Kotu Ta Daure Dillalin Tabar Wiwi Shekara 10 A Kano

Idris, ya ce wasu ‘yan jaridar ma sun rasa rayukansu wurin aikinsu.

A kan haka ya ce zai yi iyakar kokarinsa domin inganta rayuwar ‘yan jarida a gwamnatance.

“Za mu yi kokarin ganin ana bai wa ‘yan jarida dukkan hakkokin da suka cancanta a ba su.

Labarai Masu Nasaba

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

“Saboda suna aiki a cikin mawuyacin yanayi, wani lokaci ma har rasa rayukansu suke yi, kamar yadda jami’an tsaro ke rasa nasu rayukan wajen tabbatar da tsaro.

“Sau da yawa za ku ga ‘yan jarida kafada da kafada a cikin jami’an tsaro idan sun fita yaki da ta’addanci. Da dama a cikin su kan koma gida da raunuka a jikinsu.

“Kuma kun dai ga yadda dan jarida ya rasa ransa a Zamfara saboda hare-haren ‘yan bindiga.

“To duk irin wadannan ba abubuwan jin dadin ba ne a ce a matsayina na Ministan Yada Labarai na faruwa. Ina so na ga karshen wannan matsalar.,” in ji Idris.

Sannan kuma ya kawo hanzarin dalilin da ya sa gwamnati ba za ta tsame ‘yan jarida ta yi masu karin albashi su kadai ba.

Ya ce akwai muhimmancin a duba ainihin yadda aikin nasu ke da tasiri da hatsari, domin a magance matsalolin da suke fuskanta.

“Ni a sahun gaba na ke na masu hankoron ganin rayuwar ‘yan jarida ta inganta. Kuma ina taka-tsantsan da sanin cewa suna aiki ne cikin da’irar iyakar gejin tattalin arziki kasarmu.

“Don haka ya zama tilas mu dubi wannan lamari baki daya, domin a karshe a yi mana kyakkyawar shaidar ‘yan kasa nagari.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Dasa Wa ‘Yan Nijeriya Dabi’ar Gaskata Kalaman Shugabanni A Zukatansu – Minista

Next Post

Xi Ya Sanar Da Matakai 8 Na Tallafawa Raya Hadin Gwiwar Shawarar BRI Mai Inganci

Related

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

2 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

3 hours ago
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

12 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

13 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

14 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

15 hours ago
Next Post
Xi Ya Sanar Da Matakai 8 Na Tallafawa Raya Hadin Gwiwar Shawarar BRI Mai Inganci

Xi Ya Sanar Da Matakai 8 Na Tallafawa Raya Hadin Gwiwar Shawarar BRI Mai Inganci

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.