• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Jarida Sun Cancanci Samun Rayuwa Mai Inganci A Nijeriya – Minista

by Bello Hamza
2 years ago
Minista

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ‘yan jarida a Nijeriya suna aiki a cikin mawuyacin yanayi, kuma sun cancanci samun ingantacciyar rayuwa, yadda za su samu damar gudanar da ayyukansu cikin sauki da walwala.

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris ne, ya bayyana haka a wata tattaunawa da ya yi da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), a Abuja.

  • Kada Ku Bari ‘Yan Bindiga Su Shafe Baki Daya – Baraje
  • Kotu Ta Daure Dillalin Tabar Wiwi Shekara 10 A Kano

Idris, ya ce wasu ‘yan jaridar ma sun rasa rayukansu wurin aikinsu.

A kan haka ya ce zai yi iyakar kokarinsa domin inganta rayuwar ‘yan jarida a gwamnatance.

“Za mu yi kokarin ganin ana bai wa ‘yan jarida dukkan hakkokin da suka cancanta a ba su.

LABARAI MASU NASABA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

“Saboda suna aiki a cikin mawuyacin yanayi, wani lokaci ma har rasa rayukansu suke yi, kamar yadda jami’an tsaro ke rasa nasu rayukan wajen tabbatar da tsaro.

“Sau da yawa za ku ga ‘yan jarida kafada da kafada a cikin jami’an tsaro idan sun fita yaki da ta’addanci. Da dama a cikin su kan koma gida da raunuka a jikinsu.

“Kuma kun dai ga yadda dan jarida ya rasa ransa a Zamfara saboda hare-haren ‘yan bindiga.

“To duk irin wadannan ba abubuwan jin dadin ba ne a ce a matsayina na Ministan Yada Labarai na faruwa. Ina so na ga karshen wannan matsalar.,” in ji Idris.

Sannan kuma ya kawo hanzarin dalilin da ya sa gwamnati ba za ta tsame ‘yan jarida ta yi masu karin albashi su kadai ba.

Ya ce akwai muhimmancin a duba ainihin yadda aikin nasu ke da tasiri da hatsari, domin a magance matsalolin da suke fuskanta.

“Ni a sahun gaba na ke na masu hankoron ganin rayuwar ‘yan jarida ta inganta. Kuma ina taka-tsantsan da sanin cewa suna aiki ne cikin da’irar iyakar gejin tattalin arziki kasarmu.

“Don haka ya zama tilas mu dubi wannan lamari baki daya, domin a karshe a yi mana kyakkyawar shaidar ‘yan kasa nagari.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
Manyan Labarai

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
Labarai

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano
Manyan Labarai

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Next Post
Xi Ya Sanar Da Matakai 8 Na Tallafawa Raya Hadin Gwiwar Shawarar BRI Mai Inganci

Xi Ya Sanar Da Matakai 8 Na Tallafawa Raya Hadin Gwiwar Shawarar BRI Mai Inganci

LABARAI MASU NASABA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.