• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Damu Kan Yadda Kayan Masarufi Ke Tashin Gwauron Zabi

by Abubakar Abba
2 years ago
Kayan Masarufi

‘Yan Nijeriya sun damu da halin da suka tsinci kansu na ci gaba da fuskantar hauhawan farashin kayan abinci. 

Hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ta bayyana cewa hauhawar farashin kayan abinci daga shekara zuwa shekara na kara ta’azzara.

  • Kotu Ta Daure Wata Mata Kan  Zargin Kashe Mijinta A Oyo
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Manomi A Nasarawa

A cewar NBS, hauhawar farashin kayan abinci, ya karu da kashi 22.22 a cikin dari a cikin watan Afirilun 2023.

A baya farashin kwandon tumaturi ya kai daga Naira 90,000 zuwa Naira 100,000, sabanin yadda a baya ake sayar da kwandon sa daya akan Naira 20,000.

Har ila yau, farashin kwandon tattasai wanda a baya ake sayarwa akan Naira 12,000 zuwa Naira 15,000, a yanzu ana sayar da shi Naira 40,000 zuwa Naira 45,000.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Sauran kayan abincin kamar su taliyar leda mai dauke da guda 20 duk katan daya ana sayar da ita kan Naira 10,200.

Haka taliyar ‘yan yara mak dauke da guda 40 a cikin leda, ana sayar da duk katan daya kan Naira 8,000.

Baya ga hauhawar farashin kayan abincin da ake ci gaba da fuskanta, an kuma danganta tashin gwaron zabin kayan abincin akan tsadar farashin man fetur da faduwar darajar Naira da kuma karancin kayan aikin gona.

Wadannan matsalolin da aka zayyano, kari da kalubalen rashin tsaro a kasar nan sun kara jefa musamman talakawan kasar nan a cikin halin kuncin rayuwa.

A daya bangaren, wasu daga cikin manoman kasar nan, na ci gaba da fuskantar tsadar farashin kayan aikin noma, musamman saboda tsadar farashin takin zamani da magungunan kashe kwari da rashin samun ingantaccen irin noma da kuma rashin samar masu da kyayawan tsari, don yin noman rani.

Wani magidanci dan shekara 47 mai suna Emmanuel Ikechukwu da ke zaune a yankin Orozo da ke Abuja, wanda kuma yake da iyalai shida, ya bayyana cewa wannan ne karo na farko a rayuwarsa da ya taba fuskantar matsin ruyuwa da ta hade masa da hauhawar farashin kayan abinci da tsadar sufuri.

Wasu magidantan na ta hakilon samar wa iyalansu abin da za su ci, amma farashin kayan abincin, sai kara hauhawa yake yi.

Wasu gidajen da dama sun rage yawan kayan abincin da suke sayawa ahalinsu, haka sun dakatar da sayen manya kayan more rayuwa da suka saba siya.

Wani malamin makaranta mai suna Mallam Abubakar Usman, wanda ke zaune a yankin Karu a Abuja, shi ma kokawa ya yi akan hauhawan farashin kayan abincin.

Abubakar, ya ce “A yanzu haka ni da dan uwana, muna tsallake cin abinci har da ‘ya’yana uku saboda tashin gwaron zabin na kayan masarufin.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Next Post
Matsalolin Tsaro Sun Kusa Zama Tarihi A Nijeriya– Gwamna Buni

Ana Rade-Radin Bullar Cutar 'Diphtheria' A Garin Potiskum Na Jihar Yobe

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.