• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 2 Da Ceto Mutum 1 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 2 Da Ceto Mutum 1 A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu nasarar hallaka wasu mutum biyu da ake zargin ‘yan garkuwa da mutane ne sa’ilin da suka yi yunkurin garkuwa da wani mutum mai suna Usman Abdulhamid.

 

A wata sanarwar manema labarai da kakakin hukumar, SP Ahmed Mohammed Wakil ya fitar tare da raba wa ‘yan jarida a Bauchi ranar Lahadi, ya shaida cewar a bisa kokarinsu da himmarsu na dakile ta’addanci ne suka samu wannan nasarar.

  • Atiku Abubakar Ya Doke Tinubu, Obi Da Kwankwaso A Bauchi

Ya ce, a ranar 3 ga watan Maris wasu ‘yan bindiga suka mamaye gidan Alhaji Abdulhamid Muhammad da ke kauyen Rafin Cora a karamar hukumar Ningi domin su yi garkuwa da dansa mai suna Usman Abdulhamid dan shekara 28 a duniya.

Masu garkuwa

Labarai Masu Nasaba

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

A kan hakan, shi Usman ya jajirce tare da tirjijewa, lamarin da har sai da ta kai masu garkuwan sun bude masa ruwan harsasai a cikinsa a lokacin da ya yi kokarin guje musu.

 

Wakil ya kara da cewa, “Cikin hanzari daga samun rahoton faruwar lamarin, hadakar jami’an ‘yansanda da ‘yan Bijilante a karkashin jagorancin DPO din Ningi, inda suka nausa zuwa wajen da abun ya faru domin taka wa masu garkuwan burki. Amma isarsu ke da wuya ‘yan garkuwa suka marabcesu da harbe-harbe.”

 

A matsayin maida martani, ‘yansandan su ma sun bude wuta ga masu garkuwan inda aka yi bata-kashi a tsakani.

Masu garkuwa

Ya ce, “Bisa shan karfinsu da ‘yansanda suka yi, biyu daga cikin masu garkuwan sun mutu, an kuma kwato bindiga kirar AK47 guda daya a wajen da aka fafatan.”

 

Ya kara da cewa, an samu nasarar ceto wanda suka yi kokarin garkuwa da shi tare da kaisa zuwa asibitin gwamnatin tarayya da ke Birnin Kudu a jihar Jigawa domin nema masa kulawar likitoci.

 

“Tunin kuma aka dukufa wajen bin sawun masu garkuwa da mutanen domin tabbatar da an kamo su don su fuskanci shari’a,” Wakil din ya kara da fadi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cika Alkawari Tushe Ne Ga Aiwatar Da Mulki

Next Post

Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

Related

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

5 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

3 hours ago
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
Manyan Labarai

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

4 hours ago
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
Labarai

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

5 hours ago
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

7 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
Manyan Labarai

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

10 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

LABARAI MASU NASABA

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

June 19, 2025
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

June 19, 2025
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

June 19, 2025
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

June 19, 2025
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.