• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

by Yusuf Shuaibu
5 hours ago
in Labarai
0
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun kula yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya bayyana cewa sama da yara miliyan 2.9 a Nijeriya ke fama da rashin abinci mai inganci.

Wakiliyar UNICEF a Nijeriya, Misis Cristian Munduate, ta bayyana haka a Ilorin, babban birnin Jihar Kwara, ta bayyana cewa dole ne a kai yaran da abin ya shafa zuwa asibiti domin samun kulawar gaggawa don guje wa mutuwar far-daya.

  • Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba
  • Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

Cristian Munduate bayyana hakan ne a a lokacin kaddamar da shirin samar da abinci mai gina jiki 40,000, ta amfani da asusun yara na Majalisar Dinkin Duniya. Ya kara da cewa fiye da kashi 40 cikin 100 na yaran a Jihar Kwara suna fama da wannan matsalar.

Wakiliyar UNICEF ta ce gwamnatin Jihar Kwara ta bayar da dala 100,000 ga asusun samar wa yara abinci mai gina jiki, tana mai lura cewa UNICEF ta kawo irin wannan kudade wanda adadinsu ya kai na dala 100,000.

Ta ce, “Daga bayanan da muka samu, yara 2.9 a Nijeriya na fama da rashin abinci mai gina jiki, wannan ba abun ci gaba ba ne. Don haka, ra’ayina shi ne a dauki yaran da abin ya shafa nan take zuwa asibiti don samun kulawar lafiya da gaggawa domin hana mutuwa a kan lokaci.

Labarai Masu Nasaba

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

UNICEF ta gabatar da asusun abinci na yara don karfafa zuba jari a cikin manufofi da shirye-shirye. UNICEF ta jajirce wajen yin hadin gwiwa da gwamnatin Jihar Kwara don yaki da rashin abinci mai gina jiki, musamman a lokacin kwana 1000 na farko na rayuwar yara.

“Kalubalen shi ne, yawan yara fiye da kashi 40 cikin 100 suna da gwannan matsala kuma kusan yara 300,000 suna fuskantar samun kulawar gaggawa don magance wadannan matsaloli.”

Ta danganta dalilan rashin abinci mai gina jiki ga sakamakon talauci, canjin yanayi, rashin samun abinci, da kuma matsalolin tsaro.

A nasa jawabin, Gwamna Jihar Kwara, AbdulRaman AbdulRazak, wanda ya samu wakilcin Sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Jubril Shaaba Mamman, ya bayyana cewa, tasiri mai kyau game da rayuwar yara na Jihar Kwara shi ne, samun abinci mai gina jiki, wanda wannan ya sa aka yanke shawarar karbar shirin asusun samar da abinci mai gina jiki ga yara na UNICEF.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Yara
ShareTweetSendShare
Previous Post

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

Next Post

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Related

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 
Labarai

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

10 hours ago
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal
Labarai

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

10 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

12 hours ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

15 hours ago
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

18 hours ago
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
Ilimi

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

1 day ago
Next Post
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana'antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

LABARAI MASU NASABA

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.