• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Mutane Shi Ne Kasuwa

by CMG Hausa
2 years ago

Yayin da karin kasashen Afirka ke zurfafa cudanyar cinikayya da kasar Sin, masharhanta na kara bayyana kwarin gwiwa game da fatan shigar karin hajojin nahiyar Afirka cikin babbar kasuwar Sin. Musamman ma a wannan gaba da kamfanonin sassan biyu ke kara fadada alaka, da lalubo sabbin damammakin cin gajiya daga arzikin babbar kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya.

Yanzu haka, katafariyar kasuwar Gaoqiao dake birnin Changsha, ta zamo babban sansanin baje hajojin albarkatun gona daga kasashen Afirka, tare da bazuwarsu zuwa dukkanin sassan kasar Sin. Ana iya cewa, hakan sakamako ne na managarcin tsarin cudanyar cinikayya tsakanin Sin da kasashen na Afirka, karkashin shawarar nan ta ziri daya da hanya daya, da kuma manufofin bude kofa da Sin ke yi ga sauran sassan kasa da kasa. Baya ga tanade-tanaden dake kunshe cikin manufofin hadin gwiwar Sin da Afirka na dandalin FOCAC.

  • An Yaba Da Hadin Kan Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Na Kasar Sin A Ayyukan Jin Kai Na MDD

Daya daga cikin fannoni mafiya muhimmanci da kasashen Afirka ke cin kasuwar kasar Sin a baya bayan nan shi ne cinikayyar albarkatun gona, inda ko da a baya bayan nan ma manoman kasar Kenya, suka samu zarafi na shigar da nauoin furannin daban daban cikin wannan babbar kasuwa ta kasar Sin.

Wannan kari ne kan wasu nauin mai da ake tatsa daga wasu tsirrai, wanda shi ma ake kawowa daga Madagascar, da gahawar kasar Habasha, wadanda dukkanin su ke samun karin kasuwa a Sin.

A halin da ake ciki, akwai karin kamfanonin Afirka dake kafa rassan su, tare da gudanar da hada-hadar cinikayya a kasuwar Gaoqiao dake birnin Changsha.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

Ga karin manoman kasashen Afirka dake fatan shigar da albarkatun gona cikin kasuwannin kasar Sin, muna iya cewa dama ta samu, domin kuwa kasuwar kasar wadda ke kara fadada a halin yanzu tana da tagomashi, da yanayi mai kyau na bunkasa, wanda hakan zai baiwa manoman kasashen Afirka karin damammaki na samun alherai, bayan shafe tsawon lokaci suna dogaro kadai ga kasuwannin Turai da Amurka.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki
Daga Birnin Sin

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Next Post
Wata Sabuwar Cuta Ta Kashe Yara 10 ‘Yan Kasa Da Shekara 13 A Kaduna 

Wata Sabuwar Cuta Ta Kashe Yara 10 'Yan Kasa Da Shekara 13 A Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.