• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Fitar Da Karin Sunayen Ministoci –Gbajabiamila

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Za A Fitar Da Karin Sunayen Ministoci –Gbajabiamila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, ya ce da yiyuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta kirkiro wasu sabbin ma’aikatu da za su zama kari kan wadanda ake da su. 

Femi ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis a Abuja, inda ya ce bayan jerin ministoci 28 da Tinubu ya gabatar, zai kuma sake aikewa da sunayen mutum 13 nan gaba kadan.

  • Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes
  • Gwamman Zamfara Ya Karrrama Hajiyar Da Ta Tsinci Dala 80,000 A Saudiyya

Ya ce, ministocin da aka gabatar sai da suka tsallake tantancewar shugaban kasa da kansa.

Ya ce ba ya ga sunan mutum 28 da Tinubu ya gabatar a matsayin ministoci, zai kuma sake aikewa da kashi na biyu na ministocin da suka kunshi sunayen mutum 13.

“Kamar yadda kuka sani kwanaki 60 da rantsuwa, kamar yadda yake kunshe cikin kundin tsarin mulki. Ya cika ka’idar ya gindaya ta hanyar tura sunayen mutum 28 a yau.

Labarai Masu Nasaba

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

“Kamar yadda aka karanta cikin wasikarsa a gaban majalisar dattawa, akwai karin sunayen da za a gabatar, babu tabbacin su nawa ne amma wakila za su haura 12, za a tura sunayen ga majalisar dattawa nan da ‘yan kwanaki.”

Kamfanin Dillacin Labarai (NAN) ta ruwaito cewa Gbajabiamila ne ya gabatar da jerin sunayen ministocin da Tinubu ya zaba kuma shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya karanta a majalisar.

Ministocin da aka zaba 28 su ne: Abubakar Momoh, Yusuf Maitama Tuggar, Ahmed Dangiwa, Hannatu Musawa, Chif Uche Nnaji, Dokta Betta Edu, Dokta Doris Aniche Uzoka, David Umahi da Nyesom Wike.

Sauran su ne Badaru Abubakar, Nasiru Ahmed El-Rufai, Ekperipe Ekpo, Nkeiruka Onyejocha, Olubunmi Tunji Ojo, Stella Okotette, Uju Kennedy Ohaneye, Mista Bello Muhammad Goronyo, Mista Dele Alake, da Mista Lateef Fagbemi.

Akwai kuma Mista Muhammad Idris, Mista Olawale Edun, Mista Waheed Adebayo Adelabu, Misis Iman Suleiman Ibrahim, Farfesa Ali Pate, Farfesa Joseph Utsev, Sanata Abubakar Kyari, Sanata John Enoh, da kuma Sanata Sani Abubakar Danladi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MinistociMukamiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes

Next Post

Kutsen Yanar Gizo Da Take Kaiwa Sin Ya Shaida Damuwar Amurka A Fannin Tsaro

Related

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

24 hours ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

2 days ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

2 days ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

2 days ago
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

2 days ago
Next Post
Kutsen Yanar Gizo Da Take Kaiwa Sin Ya Shaida Damuwar Amurka A Fannin Tsaro

Kutsen Yanar Gizo Da Take Kaiwa Sin Ya Shaida Damuwar Amurka A Fannin Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.