Za a gudanar da taron shekara-shekara na sabbin masu jagoranci karo na 16 na dandalin tattalin arzikin duniya na lokacin zafi wato DAVOS a takaice, a birnin Tianjin dake gabashin kasar Sin, bisa taken “Ruhin ’yan kasuwa a sabon zamani”.
An shirya tsaf game da wannan taro don maraba da zuwan wakilai fiye da 1800 daga yankuna ko kasashen da suka zarce 90, inda adadin mahalarta taron na wannan karo zai kai matsayin koli a shekarun baya-bayan nan.
An ce, taron na wannan karo zai kunshi abubuwa masu dimbin yawa, bisa yadda za a gudanar da kananan taruruka kimanin 200, inda za a tattauna kan yanayin tattalin arzikin duniya da hangen nesa kan makomar Sin da bunkasar mabambantan sana’o’i a cikin manyan sauye-sauye da kuma zuba jari kan bil Adam da duniyarmu, kana da sabbin makamashi.
Ban da wannan kuma, taron a wannan karo zai dora muhimmanci sosai kan ra’ayin samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, inda za a samar da wutar lantarki ga taron bisa makamashi mai tsabta da kashi 100%, matakin da zai rage fitar da hayaki mai gurbata yanayi na Carbon Dioxide kimanin ton 600. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp