• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Gyara Wuta A Inganta Lafiya Da Ilimi Da Kuɗin Tallafin Lantarkin Da Aka Janye – Ministan Labarai 

bySulaiman
1 year ago
inLabarai
0
Wuta

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce sama da naira tiriliyan 1 da za a tara daga janye tallafin wutar lantarki za a sake zuba su ne wajen inganta wutar lantarki, kiwon lafiya, da ilimi ga ‘yan Nijeriya.

Da yake jawabi a matsayin babban baƙo na shahararren shirin Rediyo Nijeriya na Kaduna mai suna ‘Hannu Da Yawa’ a ranar Asabar a Kaduna, Idris ya ce a kusan kashi 40 na tallafin wutar lantarki, kashi 15 ne kawai masu amfani da wutar lantarki ke amfana wanda ya ƙunshi mawadata da gungun masana’antu, waɗanda ke jin daɗin wutar lantarki na kusan awanni 20.

  • Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Japan Ke Daukar Wasu Matakan Da Ka Iya Haifar Da Hadari?
  • Yanzu-yanzu: Hatsaniya Ta Kaure Tsakanin Sojoji Da Matasa A Gashuwa

Ya ce, “Yana da muhimmanci a jaddada cewa kuɗaɗen da za a ajiye daga janye tallafin wutar lantarki, za a sake zuba su ne wajen inganta samar da wutar lantarki a faɗin ƙasar nan da inganta sauran muhimman ayyukan jama’a kamar kiwon lafiya da ilimi. Kusan kashi 85 cikin ɗari na al’ummar da ke cikin sabon tsarin samar da wutar lantarki har yanzu suna samun tallafin.”

Ministan ya ce sabuwar dokar samar da wutar lantarki da Shugaban Ƙasa Tinubu ya sanya wa hannu ta ƙara ƙarfafa tsarin gudanar da ayyukan Hukumar Kula Da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC) tare da bai wa hukumar damar sanya wa kamfanonin rarraba wutar lantarkin (DISCOs) tsauraran takunkumi kan laifukan da suka shafi kuɗi da samar da wutar ga masu amfani.

Idris ya kuma bayyana cewa kwamitin da Shugaban Ƙasa ya kafa domin duba tsarin tafiyar da Shirin Zuba Jarin Jama’a na Ƙasa ya gabatar da rahotonsa domin share fagen sake gudanar da shirye-shiryen, wanda zai bayar da tallafin kuɗi naira 25,000 ga talakawa miliyan 15 da magidanta masu rauni na tsawon watanni uku a tsakanin sauran ayyukan.

Labarai Masu Nasaba

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

Ministan, wanda ya yi amfani da wannan dandali wajen kawar da maganar da wasu ke yi cewa wai gwamnatin Tinubu na shirin cutar da arewacin ƙasar nan, ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da zuba kuɗaɗe wajen bunƙasa ayyuka a Arewa.

Ya yi nuni da cewa gwamnatin ta faɗaɗa noman alkama, shinkafa, rogo, da masara, a ƙarƙashin Shirin Noman Rani zuwa kadada 500,000 na gonaki.

Ya ce: “Shugaban Ƙasa ya umarce mu da mu fito mu ji halin da al’umma ke ciki, mu kawo masa rahoto. Mun je Dutse, Auyo, da Haɗeja, kuma mun tattauna da manoma game da nasarorin noman rani a waɗannan yankuna”.

Idris ya bayyana jin daɗin sa kan yadda a yanzu Jihar Kebbi ta zama cibiyar noman tumatur da sarrafa tumatur a ƙasar nan ta hanyar haɗin gwiwa da wani babban kamfanin sarrafa abinci mai suna GB Foods, wanda ya kafa wata masana’anta domin noman tumatur.

Ya ce manoma da dama, waɗanda galibin su mata ne, yanzu haka su na noman tumatur a Jihar Kebbi, saboda yanayin da ake samu da kuma tallafi daga GB Foods, wanda ya nuna matuƙar jajircewa wajen yin kasuwanci a Nijeriya.

ShareTweetSendShare
Sulaiman

Sulaiman

Related

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 
Manyan Labarai

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

8 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

12 hours ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Labarai

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

14 hours ago
Next Post
Aisha Galadima

DSS Ta Kama Abokiyar Siyasar El-rufai, Aisha Galadima

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

October 6, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Tinubu

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

October 6, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

October 6, 2025
Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.