• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kara Bunkasa Hadin Gwiwar Tsaro Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
Afirka

Da yammacin yau Alhamis ne aka gudanar da taron manema labarai, a ma’aikatar tsaron kasar Sin, inda kakakin ma’aikatar kanar Zhang Xiaogang, ya ce a shekarun baya bayan nan, alakar harkokin soji tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka na kara zurfafa. Kaza lika sassan biyu, sun gudanar da dandalin zaman lafiya da tsaro, da taron musamman kan hakan, suna kuma ci gaba da yin musaya ta kut da kut a dukkanin matakai.

Zhang, ya kara da cewa, Sin da kasashen Afirka sun ci moriyar hadin gwiwa a sassa kamar na gina tsarin aikin soji, da horas da dakaru, da tsaron teku, da ayyukan wanzar da zaman lafiya, da bunkasa kiwon lafiya, da ayyukan ceton jin kai da na dakile bala’u.

  • GDPn Kasar Sin Na Shekarar 2023 Ya Karu Da Kashi 5.2 Cikin Dari
  • Sin Ta Kira Taron Tattauna Kan Rahoton Gwamnati

Jami’in ya ce rundunar sojin Sin za ta ci gaba da daukaka akidun gaskiya,

da cimma sakamako na zahiri, da tabbatar da tafiya tare, da amincewa juna, da aiki tare da sauran rundunonin sojin kasashen Afirka, wajen ingiza aiwatar da muhimman manufofi da jagororin su suka cimma matsaya a kai. Har ila yau, sassan biyu za su karfafa tuntubar juna bisa matsayin koli, da hadin gwiwa na zahiri.

A daya hannun za su kara inganta hadin gwiwa mai ma’ana da karko, da samar da tabbacin aminci na tsaro, ta yadda za a gina al’umma mai makomar bai daya bisa matsayin koli tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da bayar da babbar gudummawa ta wanzar da tsaron yankuna da duniya baki daya, da yayata gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil Adama.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Don gane da aiwatar da tsarin rakiyar jiragen ruwa, da rundunar sojin ruwan Sin ke gudanarwa a tekun Aden da yankunan ruwan Somalia kuwa, Zhang Xiaogang ya ce wannan batu ne wanda ba shi da wata nasaba da halin da ake ciki yanzu haka a yankin. Don haka Sin za ta ci gaba da aiwatar da manufofin tsaron kasa da kasa, da tabbatar da kariya a hanyoyin tekunan kasa da kasa, da samar da tsarin sufurin teku abun dogaro, wanda zai ci gaba da rake jiragen ruwan Sin da ma na sauran kasashe. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

October 31, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

October 31, 2025
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
Next Post
Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

October 31, 2025

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

October 31, 2025
Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai

October 31, 2025
Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

October 31, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

October 31, 2025
Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

October 31, 2025
Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

October 31, 2025
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.