• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kara Bunkasa Hadin Gwiwar Tsaro Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Za A Kara Bunkasa Hadin Gwiwar Tsaro Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin yau Alhamis ne aka gudanar da taron manema labarai, a ma’aikatar tsaron kasar Sin, inda kakakin ma’aikatar kanar Zhang Xiaogang, ya ce a shekarun baya bayan nan, alakar harkokin soji tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka na kara zurfafa. Kaza lika sassan biyu, sun gudanar da dandalin zaman lafiya da tsaro, da taron musamman kan hakan, suna kuma ci gaba da yin musaya ta kut da kut a dukkanin matakai.

Zhang, ya kara da cewa, Sin da kasashen Afirka sun ci moriyar hadin gwiwa a sassa kamar na gina tsarin aikin soji, da horas da dakaru, da tsaron teku, da ayyukan wanzar da zaman lafiya, da bunkasa kiwon lafiya, da ayyukan ceton jin kai da na dakile bala’u.

  • GDPn Kasar Sin Na Shekarar 2023 Ya Karu Da Kashi 5.2 Cikin Dari
  • Sin Ta Kira Taron Tattauna Kan Rahoton Gwamnati

Jami’in ya ce rundunar sojin Sin za ta ci gaba da daukaka akidun gaskiya,

da cimma sakamako na zahiri, da tabbatar da tafiya tare, da amincewa juna, da aiki tare da sauran rundunonin sojin kasashen Afirka, wajen ingiza aiwatar da muhimman manufofi da jagororin su suka cimma matsaya a kai. Har ila yau, sassan biyu za su karfafa tuntubar juna bisa matsayin koli, da hadin gwiwa na zahiri.

A daya hannun za su kara inganta hadin gwiwa mai ma’ana da karko, da samar da tabbacin aminci na tsaro, ta yadda za a gina al’umma mai makomar bai daya bisa matsayin koli tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da bayar da babbar gudummawa ta wanzar da tsaron yankuna da duniya baki daya, da yayata gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil Adama.

Labarai Masu Nasaba

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Don gane da aiwatar da tsarin rakiyar jiragen ruwa, da rundunar sojin ruwan Sin ke gudanarwa a tekun Aden da yankunan ruwan Somalia kuwa, Zhang Xiaogang ya ce wannan batu ne wanda ba shi da wata nasaba da halin da ake ciki yanzu haka a yankin. Don haka Sin za ta ci gaba da aiwatar da manufofin tsaron kasa da kasa, da tabbatar da kariya a hanyoyin tekunan kasa da kasa, da samar da tsarin sufurin teku abun dogaro, wanda zai ci gaba da rake jiragen ruwan Sin da ma na sauran kasashe. (Mai fassara: Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dole Ne Amurka Ta Yi Watsi Da Manufar Hana Bunkasuwar Sin

Next Post

Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

Related

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
Daga Birnin Sin

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

16 minutes ago
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

20 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

21 hours ago
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

22 hours ago
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

2 days ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

2 days ago
Next Post
Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

August 11, 2025
Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.