• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

by Khalid Idris Doya
3 weeks ago
in Labarai
0
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kamfanin Man Fetur na kasa NNPCL, Bayo Ojulari, ya sanar da shirye-shiryen dawo da ayyukan ci gaba da neman Man a Kolmani, da ke a yankin Arewa maso Gas.

Idan za a iya tunawa, a ranar 22 na watan Nuwambar 2022 ne, tsohuwar Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ta kaddamar da aikin hako Man na Kolmani, wanda aikin ya kasance, shi ne na farko da aka fara gudnarwa a Arewacin kasar.

  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Ojulari wanda ya sanar da hakan a hirarsa da kafar BBC a ranar Litinin ya yi kira ga alumomin da ke a yankin na Arewa maso Gabas da su kawantar da hankulansu tare da ba su tabbacin cewa, za a sake dawo da aikin na neman Man a Kolmani da ke a yankin Arewa maso Gabas.

“Zamu dawo da aikin na neman Man a Kolmani da kuma a sauran guraren da ake hasashen akwai Man Fetur din, baya ga batun neman Man, mun kuma mayar da hankali wajen kammala aikin sanya Bututun Danye daga Ajaokuta zuwa jihar Kano,” Inji Ojulari.

Ya sanar da cewa, wadannan ayyukan, za su taimaka wajen sake dawo da masana’antu da durkushe da kuma sake kafa wasu sabbin masana’antu.

Labarai Masu Nasaba

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

“Wannan ci gaban zai kuma taimaka wajen kara habaka tattalin ardikin da ke a yankin na Arewa maso Gabas, wanda hakan ya zame mana wajbi, mu sake dawo wajen yin aikin domin aikin ya ci gaba da tafiya,” A cewar Ojulari.

Kan batun rikicin da yaki ci, yaki cinyewa a tsakanin Kamfanin na NNPCL da kuma rukunomin Kamfanin Dangote Ojulari ya bayyana cewa, ana ci gaba da kokari domin a kawo karshen rikicin.

“Dangote ya bayar da gagarumar gudunmawa wanda kuma, ya cannaci a yaba masa, za mu kuma yi hadaka domin mu tabbatar da, mun ci gaba da samar da wadataccen Man Fetur ga ‘yan kasar nan,” Inji Sabon Shugaban.

“Ana samun masalaha kan komai ne, ta hanyar tattaunawa za mu yi aiki kafada da kafada, domin amfanin ‘yan Nijeriya,” A cewar Ojulari.

Kazalika, da yake yin tsokaci kan batun samun raguwar farashin Danyen Mai a kasuwar duniya wanda hakan ya sanya burin samun kudaden shiga na kasar ya ragu, ya sanar da cewa, hakan ya shafi kasafin kudin kasar, duba da cewa, akasarin hasashen kasar ya dogara ne, kan samun kudin shiga na Man.

Ya sanar da cewa, NNPCL na kan aikin rage kashe kudaden gudanar da ayyukansa, wanda hakan zai bai wa Kamfanin damar yin amfani da kudaden shigar da yake samu, ta hanyar sayar da Man Fetur da na Iskar Gas.

Kan korafin da wasu yan kasar ke yi, kan rashin raguwar farashin Man Fetur da ake sayarwa a kasar, duk da cewa, farashinsa ya ragu a kasuwar duniya ya ce, Dilolin Man na bukatar lokaci, domin rage farashinsa.

“Idan Dilalan sun sayi Man kafin farashinsa ya ragu, suna bukatar su sayar da shi ne, kan tsohon farashi, amma idan sun saye shi kasa da sabon farashi, muna sa ran farashin ya sauka wanda zai nuna cewa, an samu sauyi,” Inji Ojulari.

A cewar NNPCL, tarin aikin na neman Man na Kolmani, an faro shi ne, tare da Kamfanin Mai na Shell a 1970, amma daga baya, aka yi watsi da aikin domin ba samu wata gagarumar cimma nasara ba.

Sai dai, daga baya an sake dawo da aikin ta hanyar Kolmani Riber 2, 3, and 4 a shekarar 2019, wanda hakan ya sanya aka gano Gangunan Danyen Mai biliyan daya da kuma Iskar Gas biliyan 500.

NNPC a ya sanar da cewa, a 2019 ya sake gabata da bukatar a yi amfani da kimiyyar zamani domin a ci gaba da aikin na nemna Man Kolmani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NNPCL
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

Next Post

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

Related

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

6 minutes ago
Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
Labarai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

4 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Manyan Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

5 hours ago
Tinubu
Labarai

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

6 hours ago
jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

19 hours ago
Next Post
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

June 14, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

June 14, 2025
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

June 14, 2025
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi

June 14, 2025
Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

June 14, 2025
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

June 14, 2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

June 14, 2025
Tinubu

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

June 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

June 14, 2025
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.