• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Dasa Wa ‘Yan Nijeriya Dabi’ar Gaskata Kalaman Shugabanni A Zukatansu – Minista

by Bello Hamza
2 years ago
Gaskata

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kain Jama’a, Mohammed Idris, ya nuna damuwarsa ganin yadda akasarin ‘yan Nijeriya suka daina yin amanna ko gaskata kalaman shugabanninsu.

Ministan, ya bayyana haka a wata tattaunawa da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), a Abuja.

  • Majalisar Wakilai Za Ta Amince Da Kasafin Kudin 2024 Kafin Karshen Disamba
  • Kotu Ta Daure Dillalin Tabar Wiwi Shekara 10 A Kano

“Abin da mu ke so shi ne a bar ‘yan Nijeriya su san gaskiya daga wadanda suka wajaba su bayyana masu gaskiyar. Ina ganin muhimmin abu ne sosai a ga cewa an dora tsarin isar da sako a kan turbar fada ko bayyana gaskiya, ta yadda wanda ake fada wa gaskiyar zai yi amanna da abin da mai fada masa gaskiyar ya ke fada.

“Wannan haka ne, saboda mun ga irin yadda amanna da gwamnati da kuma amincewa suka gushe ko suka zaizaye a zukatan jama’a, a kasar nan.

“Mun kai matakin da akasarin ‘yan Nijeriya ba su yi amanna da abin da shugabanninsu ke fada musu ba. Kuma su mutanen su ne suka zabi shugabannin da hannunsu.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

“Saboda haka akwai bukatar mu fara ganin mun kankaro wa wannan gwamnati daraja, ta hanyar samun amincewa da amanna daga wurin ‘yan Nijeriya.

“Za mu yi wannan aikin haikan, bakin karfi da iyawar gwamnati, domin ganin jama’a sun dawo suna gaskata kalamai da bayanan gwamnati,” cewar Idris.

Ya kara da cewa fadin gaskiya shi ne matakin farko na nagartar mutum, domin idan jama’a suka san gwamnati na fadar gaskiya, to su ma fa masu bada rahotannin bayanai tsakanin tilas su rika fadar gaskiya.

Idris ya ce gwamnati na kokarin kara zaburar da jama’a cewa kowa ya kasance yana fadar gaskiya.

“Za mu fito mu yi kamfe na dakile masu yada labaran bogi da karairayi, wadanda hatsarin su zai iya kai wa ga ruguza al’umma ko kawo rabuwar kai.

“Kuma za mu ci gaba da kwadaitar da kafafen yada labarai su tsaya kan turbar bayyana gaskiya, wadda dama ita ce kyakkyawar dabi’ar da aka san kafafen yada labarai ke kan ta, kuma suke kan koyarwar ta,” cewar Minista Idris.

Dangane da labaran bogi, Idris ya ce wannan matsala ba ta Nijeriya kadai ba ce, abu ne wanda ya game duniya.

Ya ce idan aka hada hannu za a iya kawar da yaduwar su, ba tare da an take hakkin kowa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Next Post
‘Yan Jarida Sun Cancanci Samun Rayuwa Mai Inganci A Nijeriya – Minista

'Yan Jarida Sun Cancanci Samun Rayuwa Mai Inganci A Nijeriya - Minista

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.