• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Dawo Da Martabar PDP A Katsina — Kwamitin Riƙon Ƙwarya

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
in Labarai
0
Za Mu Dawo Da Martabar PDP A Katsina — Kwamitin Riƙon Ƙwarya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar adawa ta PDP wanda uwar jam’iyyar ta turo Jihar Katsina domin daidaita al’amurra, ya ce zai mayae da hankali kan abubuwa guda uku daga cikin har da haɗa kan ‘yan jam’iyyar domin shafe tasirin sauran jam’iyyu. 

Shugaban kwamitin rikon kwaryar, Alhaji Musa A. Karim, ya bayyana haka jim kadan bayan sun kammala taro da mambobin jam’iyyar.

  • Tinubu Zai Kori Ministocin Da Ba Su Da Kwazon Aiki – Hadiza Bala Usman
  • Sanusi Ya Amince Da Mayar Da Wasu Ma’aikatun CBN Zuwa Legas

Ya ce bayan tattara hankalin ‘ya’yan jam’iyyar waje guda, za su tabbatar sun sasanta duk wani sabani da sauran bangarori da suka samu rashin fahimtar juna a baya.

“Muna da kalubale a wannan jam’iyya ta PDP a Katsina, amma hakan ba zai hana mu ba samun kwarin gwiwa wajen ganin mun dawo da martabarta a Jihar Katsina ba,” in ji shi.

Ya kara da cewa abu na uku da jam’iyya ke fuskanta shi ne zaben cike gurbi da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) za ta gudanar a watan Fabrairu, 2024, wanda ya shafi dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Sabuwa da Kankara da kuma Faskari.

Labarai Masu Nasaba

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Idan za a yi tunawa dan takarar majalisar tarayya karkashin jam’iyar APC a zaben 2023, Honarabul Dalhatu Shehu Tafoki ya kai karar Hon. Jamilu Mohammed Lion, wanda INEC ta bayyana a matsayin wanda ya lashe zaben.

Karim, ya ci gaba da cewa wannan kwamiti na rikon kwarya zai tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a zaben da za a sake.

Kwamitin na mutum 15 da suka hada da Hon. Musa A. Karim shugaban jam’iyyar PDP da Hon Sanusi Ali da Hon. Abubakar Lawal da Hon. Abubakar Yusuf da Hon. Ibrahim Assalamu Alaikum da Hon. Nura Gambo da Hon. Tijjani Mashasha.

Sauran sun hada da Hon. Ubaida Jafar da Hon. Lawal Magaji Ɗanɓaci da Hon. Danjuma Altine da Hon. Haruna Garba, (Dogo na Maraya) da Hon. Ibrahim Tafashiya da Hon. Ubaida Mai’adua da Hon. Shitu Magami da kuma Halina Zubairu Ɗanbata a matsayin sakatariyar rikon kwarya ta jam’iyyar PDP a Katsina

Jam’iyyar PDP dai a Jihar Katsina na fama da rikicin da ya kai ta ga rashin nasarar zaɓe5n gwamnan da ya gabata tare rasa wasu kujerun ‘yan majalisar tarayya a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KatsinaPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Kori Ministocin Da Ba Su Da Kwazon Aiki – Hadiza Bala Usman

Next Post

‘Yansandan Sun Ceto Mutane 14, Sun Kashe Dan Bindiga A Nasarawa

Related

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

2 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

2 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

2 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

5 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

7 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

22 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa 17 A Filato

'Yansandan Sun Ceto Mutane 14, Sun Kashe Dan Bindiga A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.