• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Gyara Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Da Ta Yanke Cikin Kwana 3

Gina Sabon Titi Ne Ya Dace Da Hanyar -  Gwamna Bala

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Za A Gyara Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Da Ta Yanke Cikin Kwana 3
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin da gwamnatin tarayya ta bai wa aikin kula da kwaskwarima na babban hanyar Bauchi zuwa Gombe, Anaco Nigeria Limited, ya sha alwashin gyara hanyar da ta yanke a daidai gadar Kaljanga cikin kwanaki uku masu zuwa. 

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa, a sakamakon mamakon ruwan sama da aka tafka a safiyar ranar Lahadi wanda ya yi sanadin ruftawar gadar, lamarin da janyo raba jihohin da ke yankin arewa maso gabas daga zuwa sauran yankunan kasar nan.

  • Matafiya Sun Makale Sakamakon Ruftawar Gada A Hanyar Gombe Zuwa Bauchi

Lamarin ya tilasta wa wasu matafiyan fasa tafiyar yayin da wasu kuma suka yi zagaye mai nisa domin samun damar zuwa wuraren da suke son zuwa.

Kodayake, kamfanin ya ce nan da kwanaki uku za su yi garanbawul ga hanyar ta yadda motoci za su samu damar wucewa.

Wakilinmu ya labarto cewa ba wannan ne karo na farko da hanyar Bauchi zuwa Gombe ke yankewa ba, sai dai ba a taba samun yankewar hanyar ba kamar na wannan lokacin.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Gwamna Bala Muhammad da ya ke maida jawabi jim kadan bayan wakilin kamfanin kwangilar ya bada tabbacin kammala kwaskwarimar cikin Kwana Uku, ya ce, wannan lamarin ya janyo kunci ga jama’a kuma zai shafi tattalin arzikin jama’a muddin ba a yi gaggawar daukar matakin gyara hanyar cikin kankanin lokaci ba.

Bala ya ce, hanyar ta gaji ne gaba daya ba ta bukatar wata kwaskiwarima, sake ginawa ne ya dace da ita.

Ya bukaci gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu da ta duba halin da hanyar ke ciki domin sake bayar da kwangilar sake ginawa, ya nuna takaicinsa kan yadda gwamnatin baya ta Muhammadu Buhari ta yi watsi da hanyar duk da tsananin bukatar agajin gaggawa da hanyar ke bukata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Sokoto Za Ta Dauki Nauyin Karatun ‘Yan Asalin Jihar 85 A Jami’ar NorthWest

Next Post

Neymar Jr Ya Koma Kungiyar Al Hilal Ta Kasar Saudiya Da Taka Leda

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

3 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

4 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

5 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

6 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

8 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

8 hours ago
Next Post
Neymar Jr Ya Koma Kungiyar Al Hilal Ta Kasar Saudiya Da Taka Leda

Neymar Jr Ya Koma Kungiyar Al Hilal Ta Kasar Saudiya Da Taka Leda

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.