• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnoni: Wasu Na Kitsa Makarkashiyar Bata Sunan Gwamnan Gombe —APC

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Zaben Gwamnoni: Wasu Na Kitsa Makarkashiyar Bata Sunan Gwamnan Gombe —APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar APC a Jihar Gombe, ya ce ya gano wasu bata-gari daga jam’iyyun adawa a jihar, na kitsa makarlashiyar bata sunan Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, dan takaran gwamna a jam’iyyar a zabe mai zuwa.

A wata sanarwar da Ismaila Uba Misilli, Daraktan yada labarun kwamitin yakin neman zaben APC A Jihar Gombe, ya ce, “Sahihan bayanai sun yi nuni da cewa wadannan ‘yan adawar su na aika-aikar su ne karkashin masu basu na goro don neman bata suna da karya lagon dan takaranmu da sauran jiga-jigan jam’iyyar domin su yaudari al’ummar Jihar Gombe wadanda tuni suka yanke shawarar sake zaben Gwamna Inuwa a karo na biyu.”

  • Siyasar Bauchi: ‘Yansanda Na Neman Dan Majalisar Tarayya, Yakubu Shehu Ruwa A Jallo
  • Na Kalubalanci Tsarin Da Ya Ayyana Tinubu A Matsayin Shugaban Kasa -Peter Obi

Ya kara da cewa, “Ganin yadda suka tabbatar cewa ba za su yi wani katabus a zaben gwamnoni da na ‘yan majalisan jiha da za a yi a ranar 18 ga wannan wata na Maris ba, wadannan makiya na Jihar Gombe sun dauki aniyar aiwatar da mummunan makircin su don ganin hakar su ta cimma ruwa.”

“Mu ‘yan kwamitin yakin neman zaben Jam’iyyar APC a Jihar Gombe mun ga ya dace mu jawo hankalin al’ummar jihar tare da yin kira a gare su, su yi watsi da duk wani makirci irin wannan.”

Ya jaddada cewa Gwamna Inuwa Yahaya ya tsaya tsayin daka da jajircewa wajen ci gaba da gudanar da mulki na gari don ingantuwar Gombe ga dokacin al’ummar jihar da kewaye.

Labarai Masu Nasaba

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

“Muna kira ga al’umma kar irin wannan zagon kasa da farfagandar siyasa na ‘yan adawa ya rude su, wadanda ke barazana ga zaman lafiyarmu.”

Ya ce, Gombe ta yi suna a fagen zaman lafiya da siyasa mai tsabta. Don haka dole ne suke fatan gudanar da harkokin zabe a matsayin ‘yan uwa ba tare da nuna kyama ko son zuciya da da”cin rai ba.

“Haka nan muna gargadin masu kitsa irin wannar makarkashiya da aika-aika, su shiga taitayin su, domin al’ummar Jihar Gombe su na goyon bayan Gwamna Inuwa Yahaya kuma da yardar Allah zasu ba shi damar yin wa’adi na biyu a ranar Asabar 18 ga wannan wata.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBata SunaGombeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Siyasar Bauchi: ‘Yansanda Na Neman Dan Majalisar Tarayya, Yakubu Shehu Ruwa A Jallo

Next Post

An Daure Matashi Shekara 1 Kan Satar Janareta A Abuja

Related

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

1 hour ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

2 hours ago
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

3 hours ago
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati
Labarai

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

5 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

6 hours ago
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
Manyan Labarai

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

15 hours ago
Next Post
An Daure Matashi Shekara 1 Kan Satar Janareta A Abuja

An Daure Matashi Shekara 1 Kan Satar Janareta A Abuja

LABARAI MASU NASABA

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

August 12, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

August 12, 2025
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

August 12, 2025
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

August 12, 2025
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

August 12, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

August 12, 2025
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.