• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zakaran Da Allah Ya Nufa Da Cara…

by CMG Hausa
3 years ago

Kasar Sin, kamar ragowar kasashe na da ikon zabar hanyoyin raya kanta bisa yanayin da take ciki, don haka, bunkasuwar kasar, kamar yadda ta sha nanatawa a mabambantan lokuta cewa, har kullum buri da manufar kasar Sin, shi ne tabbatar da ci gaba da zaman lafiyar duniya baki daya, sabanin yadda wasu kasashe ke kallonta da ma yada jita-jitar cewa, wai ci gaban kasar Sin, musamman kokarin da take na zamanantar da kanta, baraza ce ga duniya. 

Sanin kowa ne cewa, kasar Sin na da dabaru da fasahohi masu kyau a fannin ingiza zamanintarwa da hadin kan kasa da kasa, da sa kaimi ga canja salon makamashi, kuma dukkansu abin koyi ne ga kasashen duniya. Amma wasu kasashe na nuna kishi da ci gaban kasar Sin, inda suke kokarin yiwa wannan ci gaba bahaguwar fahimta tare da neman hana ci gabanta ta kowa ne hanya.

  • Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Bunkasa Da Kaso 4.8% A Rubu’in Farko Na Bana Duk Da Raguwar Bukatun Waje

Kasar Sin ta samu babban ci gaba a fannin kawar da talauci, da raya masana’antu, da yin amfani da sabbin fasahohi, kana tana da gogewa masu tarin yawa, da za ta iya rabawa ga duniya. Don haka sauran kasashe za su iya koyo da ma cin gajiya daga zamanantarwa irin na kasar.

Masu fashin baki na cewa, akwai bukatar kasashe su koyi kyawawan manufofi da ayyukan juna, yadda kasar Sin take da kwarewa da kuma musayar gogewarta, babu shakka zai taimakawa kasashe, musamman masu tasowa wajen zabar salon zamanintarwa da zai dace da yanayin kasashensu da kuma biyan bukatunsu.

A matsayinta na kasar da ta san ya kamata, Sin tana hadin kai da kasashe mambobin MDD don aiwatar da shawarar raya duniya baki daya, da kafa tawagar sada zumunta wajen aiwatar da shawarar a dandalin majalisar. Shawarar da ta nuna kyakkyawan fata da alkawarin da kasar Sin ta yi wajen inganta ci gaban duniya.

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Har kullum kasar tana fatan kasashen yammacin duniya, musamman Amurka da sauran kawayenta za su kalli ci gabanta, da kokarin da take na zamanantar da kanta da idon na basira, ta yadda za su dakatar da yada farfaganda maras tushe, ta daukar wannan manufa da masu fashin baki ke cewa, za ta amfani duniya a matsayin barazana.

Hanya mafi dacewa ta warware dukkan batutuwa da suka shafi kasashen duniya, musamman a wannan lokaci da duniya ke bukatar zaman lafiya, adalci ita ce tattaunawa, maimakon ware kai, da mayar da wasu saniyar ware, da gudanar da komai a bayyane, da damawa da kowa da kowa bisa daidaito da mutunta juna, tare da ci gaba da shawarwari da yin hadin gwiwa, maimakon yada zarge-zarge marasa tushe. Amma zakaran da Allah ya nufa da cara, ko ana muzuru ko ana shafo sai ya yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Next Post
An Sallami ‘Yan Sandan Da Ke Bai Wa Rarara Kariya Daga Aiki

An Sallami 'Yan Sandan Da Ke Bai Wa Rarara Kariya Daga Aiki

LABARAI MASU NASABA

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.