• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zakaran Da Allah Ya Nufa Da Cara…

by CMG Hausa
3 years ago

Kasar Sin, kamar ragowar kasashe na da ikon zabar hanyoyin raya kanta bisa yanayin da take ciki, don haka, bunkasuwar kasar, kamar yadda ta sha nanatawa a mabambantan lokuta cewa, har kullum buri da manufar kasar Sin, shi ne tabbatar da ci gaba da zaman lafiyar duniya baki daya, sabanin yadda wasu kasashe ke kallonta da ma yada jita-jitar cewa, wai ci gaban kasar Sin, musamman kokarin da take na zamanantar da kanta, baraza ce ga duniya. 

Sanin kowa ne cewa, kasar Sin na da dabaru da fasahohi masu kyau a fannin ingiza zamanintarwa da hadin kan kasa da kasa, da sa kaimi ga canja salon makamashi, kuma dukkansu abin koyi ne ga kasashen duniya. Amma wasu kasashe na nuna kishi da ci gaban kasar Sin, inda suke kokarin yiwa wannan ci gaba bahaguwar fahimta tare da neman hana ci gabanta ta kowa ne hanya.

  • Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Bunkasa Da Kaso 4.8% A Rubu’in Farko Na Bana Duk Da Raguwar Bukatun Waje

Kasar Sin ta samu babban ci gaba a fannin kawar da talauci, da raya masana’antu, da yin amfani da sabbin fasahohi, kana tana da gogewa masu tarin yawa, da za ta iya rabawa ga duniya. Don haka sauran kasashe za su iya koyo da ma cin gajiya daga zamanantarwa irin na kasar.

Masu fashin baki na cewa, akwai bukatar kasashe su koyi kyawawan manufofi da ayyukan juna, yadda kasar Sin take da kwarewa da kuma musayar gogewarta, babu shakka zai taimakawa kasashe, musamman masu tasowa wajen zabar salon zamanintarwa da zai dace da yanayin kasashensu da kuma biyan bukatunsu.

A matsayinta na kasar da ta san ya kamata, Sin tana hadin kai da kasashe mambobin MDD don aiwatar da shawarar raya duniya baki daya, da kafa tawagar sada zumunta wajen aiwatar da shawarar a dandalin majalisar. Shawarar da ta nuna kyakkyawan fata da alkawarin da kasar Sin ta yi wajen inganta ci gaban duniya.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Har kullum kasar tana fatan kasashen yammacin duniya, musamman Amurka da sauran kawayenta za su kalli ci gabanta, da kokarin da take na zamanantar da kanta da idon na basira, ta yadda za su dakatar da yada farfaganda maras tushe, ta daukar wannan manufa da masu fashin baki ke cewa, za ta amfani duniya a matsayin barazana.

Hanya mafi dacewa ta warware dukkan batutuwa da suka shafi kasashen duniya, musamman a wannan lokaci da duniya ke bukatar zaman lafiya, adalci ita ce tattaunawa, maimakon ware kai, da mayar da wasu saniyar ware, da gudanar da komai a bayyane, da damawa da kowa da kowa bisa daidaito da mutunta juna, tare da ci gaba da shawarwari da yin hadin gwiwa, maimakon yada zarge-zarge marasa tushe. Amma zakaran da Allah ya nufa da cara, ko ana muzuru ko ana shafo sai ya yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Next Post
An Sallami ‘Yan Sandan Da Ke Bai Wa Rarara Kariya Daga Aiki

An Sallami 'Yan Sandan Da Ke Bai Wa Rarara Kariya Daga Aiki

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.